Home General EFCC ta ba da belin tsohon gwamnan Sokoto Tambuwal da ta tsare

EFCC ta ba da belin tsohon gwamnan Sokoto Tambuwal da ta tsare

Hukumar da ke yaki da yi wa masu yi wa tattalin arzikin ƙasa zagon ƙasa a Najeriya EFCC ta bayar da belin tsohon gwamnan jihar Sokoto, Aminu Tambuwal, bayan ta yi masa tambayoyi kan wawushe dukiyar ƙasa da ya kai sama da Naira biliyan 189.

An gayyaci Tambuwal wanda ya mulki jihar Sokoto daga shekarar 2015 zuwa 2023, zuwa hedikwatar EFCC da ke Abuja ranar Litinin, inda ya isa da misalin karfe 11:30 na safe.

Masu bincike sun yi masa tambayoyi kuma daga baya aka tsare shi a shelkwatar hukumar.

Majajiyoyi sun ce, a ranar Talata, aka saki tsohon gwamnan bayan cika sharuddan belinsa, waɗanda aka bayyana a matsayin mara tsauri.

Ƴan adawa sun bayyana tsare tsohon gwamnan da EFCC ta yi, a matsayin wani yunƙuri na karya lagon ƴan adawa da gwamnati maici a ƙasar ke yi.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 200 Sun Mutu Sakomakon Girgizar ƙasar a ColombiaShahararren Mawaƙin Najeriya, Davido ya Rubuta wa Trump Wasiƙa Kan Zaɓen Jihar OsunHukumar NHRC ta Buƙaci a Kama Malamin Addinin, Sheikh JingirRundunar sojin Najeriya ta Daƙile Shirin Ƴan Bindiga a FilatoJami'an Ƴan Sanda 10 Sun Mutu Yayin Artabu da Ƴan Bindiga a Jihar KebbiAn Naɗa ɗan Najeriya Gidado Shuaib Wakilin Matasa na IPRA-UN Gabanin GWAEFCC da "Wuce Gona da Iri" da Tambayar 2027: Shin ana Rudar da Tinubu ta Hanyar Mutanen da ke Kewaye da Shi ? Daga Yushau A. ShuaibAn Samu Gawar Yara 3 da guda 1 a Sume a Gidan Mai Maganin GargajiyaMene ne Ainihin Abin da ya faru Aka Rufe Asusun Bankunan Gwamnatin Osun ?Jami'an Tsaro Sun Ceto Mutane 308 a Jihohin Arewacin Najeriya An Kama Mutane 6 da Ake Zargin da Taimaka wa Mayaƙan ISWAP a Jihar BornoZaɓen 2027: PDP ta Miƙa Sunan Jonathan ga INEC a Matsayin ɗan Takararta na Shugaban ƙasaIyanen Babban Jami'in Kula da Harkokin Kuɗaɗen ƙungiyar ISWAP Sun Miƙa Wuya ga SojojiAna Zargin Mayaƙan Boko Haram da Kashe Sojojin Nijar 14Gombe 2027: Malamai da Mambobin APC Sun yi Allah-wadai da Sukar Rarara ga Pantami
X whatsapp