Home Labarai Hukumar KAROTA ta kaddamar da kotun tafi da gidanka a jihar Kano

Hukumar KAROTA ta kaddamar da kotun tafi da gidanka a jihar Kano

Hukumar dake lura da zirga-zirgar ababan hawa ta jihar Kano KAROTA ta kaddamar da kotunan tafi da gidanka a jihar.

Wannan na cikin wata sanarwa da mai magana da yawun hukumar Abubakar Ibrahim Sharada Anipr ya aikewa PRNigeria, in da sanarwar ta ce hukumar ta dauki matakin ne don yankewa direbobi da ke karya dokar fitilun bada hannu a manyan titunan birni kano.

Da yake kaddamar da kotunan, Manajan Darakta na KAROTA, Hon. Faisal Mahmud Kabir, ya bayyana cewa wannan mataki ya biyo bayan umarnin da Gwamnan Jihar Kano, Alhaji Abba Kabir Yusuf, ya bai wa hukumar domin tabbatar da bin dokokin zirga-zirga daga direbobi da masu tukin adaidaita sahu a jihar.

Manajan Daraktan ya jaddada cewa ganin yadda gwamnatin Gwamna Abba Kabir Yusuf ta zuba makudan kudade wajen girka sabbin fitilun hasken wuta masu amfani da rana (solar), dole ne masu ababen hawa su nuna godiya ta hanyar bin doka da odar.

ya kuma Ya ja kunnen duk direban da aka kama yana karya dokar cewar jami’an KAROTA tare da hadin gwiwar jami’an tsaro za su cafke shi domin a gudanar da shari’a nan take a gaban kotun tafi-da-gidanka.

PRNigeria

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Dangote ya ƙara farashin man feturHukumar Jin dadin alhazan Kano ta sanar da ranar fara jigilar maniyatantaYadda Lakurawa suka kashe masallata a KebbiDSS ta kama jagoran ISWAP da ake nema ruwa a jallo a EdoBa mu taɓa goyon bayan musguna wa Kristoci ba - Gwamnatin NajeriyaGobara ta tashi a babban kasuwar Fika da ke jihar YobeWaye Tunji Disu: Sabon Babban Sifeton 'Yansandan NajeriyaNijar ta amince da kundin ayyukan AES na shekara ta biyuAtiku ya zargi gwamnatin Tinubu da yi wa dimokuraɗiyya zagon ƙasaGwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanci
X whatsapp