Home General Ina nan daram a Jam’iyyar NNPP – Kwankwaso

Ina nan daram a Jam’iyyar NNPP – Kwankwaso

Dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar NNPP a zaben 2023, Rabiu Musa Kwankwaso, ya karyata jita-jitar cewa yana shirin komawa APC ko shiga sabuwar kawance a jam’iyyar ADC.

Kwankwaso ya bayyana haka ne a taron kwamitin zartarwa na jam’iyyar na kasa yau, inda ya ce zai ci gaba da kasancewa a cikin NNPP.

Jam’iyyar ta shiga rikicin shugabanci tun bayan babban taron da wani bangare ya gudanar a Fabrairu, wanda ya janyo rabuwar kawuna tsakanin magoya bayan Kwankwaso da kuma wasu daga cikin mambobin da suke ikirarin kafa jam’iyyar.

A kwanakin baya, bangaren Agbo Major ya bukaci INEC ta dage zabuka kan rikicin tambarin jam’iyyar.

Kwankwaso ya ce jam’iyyar za ta sanar da matakinta a lokacin da ya dace.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Dangote ya ƙara farashin man feturHukumar Jin dadin alhazan Kano ta sanar da ranar fara jigilar maniyatantaYadda Lakurawa suka kashe masallata a KebbiDSS ta kama jagoran ISWAP da ake nema ruwa a jallo a EdoBa mu taɓa goyon bayan musguna wa Kristoci ba - Gwamnatin NajeriyaGobara ta tashi a babban kasuwar Fika da ke jihar YobeWaye Tunji Disu: Sabon Babban Sifeton 'Yansandan NajeriyaNijar ta amince da kundin ayyukan AES na shekara ta biyuAtiku ya zargi gwamnatin Tinubu da yi wa dimokuraɗiyya zagon ƙasaGwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanci
X whatsapp