Home Labarai An bayyana jihohin arewacin Najeriya da za su iya fuskantar ambaliya a...

An bayyana jihohin arewacin Najeriya da za su iya fuskantar ambaliya a watan Satumba

Hukumar kula da madatsun ruwa ta Najeriya wato Nigeria Hydrological Services Agency (NiHSA) ta yi gargaɗin cewa aƙalla jihohin arewacin Najeriya guda 18 ne ke fuskantar barazanar ambaliya a mako biyu na farkon watan Satumban nan da aka shiga.

A wata sanarwa da hukumar ta fitar a shafinta na X, ta ce jihohin Najeriya 29 ne tare da Babban Birnin Tarayya Abuja suke fuskantar barazanar ta ambaliya a tsakanin 1 zuwa 15 ga watan Satumba.

Hukumar ta ce ambaliyar za ta iya shafar ƙananan hukumomi 107, da garuruwa 631, sannan aƙalla manyan titunan ƙasar 50 za su fuskanci tsaiko.

Daga cikin jihohin da suka fi shiga barazanar, akwai Borno da Zamfara da Jigawa da Kebbi da Yobe da Filato da Gombe da Taraba da Sokoto, sannan akwai jihar Kaduna barazanar ba ta ƙarfi sosai.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Shin AtikuObi Zasu Iya Tsige TinubuShettima a 2027? Daga Yushau A. ShuaibYadda Shari'ar Masarautar Kano ke Ci gaba da Wakana a Kotun ta ƙoliTawagar Amurka na Shirin Tafiya Pakistan Domin Tattaunawar Sulhu da IranDole Najeriya ta Samu Tsaro ta Kowane Hali - Babban Hafsan TsaroChelsea da Newcastle na Harin Coulibaly, Liverpool na Neman Siyan Marcos SensiBadaƙalar $1.3m: Kotu ta ba EFCC izinin Kama Tsohuwar Ministar jin ƙan Najeriya Sadiya FarouqRaphinha ya Magantu kan Fitar da ƙungiyarsa da aka yi Daga Champion LigRundunar sojin Najeriya ta Musanta bai wa Tsofaffin Mayaƙan Boko Haram MakamaiGwamnatin Tarayya ta Sauya Zarge-Zargen da ta ke yi wa MalamiAn Binne Birgediya Janar Braimah da Sauran Sojojin da Boko Haram ta KasheYaƙin Iran: Hauhawar farashin Kaya a Najeriya ya ƙaruAdadin Matasa 'Yan kwaya da Muka Kama a Shekara 5 - NDLEAJam'iyyar ADC ta Kori Nafi'u Bala GombeRigakafin ƙyanda ya Ceci Yara Miliyan 20 a Afirka - Hukumar Lafiya ta Duniya2027 Ita ce Dama ta ƙarshe da zan Fito Takara - Atiku
X whatsapp