Home AFIRKA Burkina Faso ta amince da dokar haramta neman maza a faɗin ƙasar

Burkina Faso ta amince da dokar haramta neman maza a faɗin ƙasar

Gwamnatin sojin Burkina Faso ta amince da wata doka da ke haramta neman maza ko luwaɗi a fadin ƙasar, wadda ta tanadi hukuncin ɗaurin shekaru 5 a gidan kaso, lamarin da ya sa ta kasance ƙasar Afirka ta baya-bayan nan da ta samar da wannan doka.

Ƙasashe kimanin 30 a nahiyar Afirka sun haramta ɗabi’ar neman maza, amma Burkina Faso ba ta yi hakan ba gabanin ƙwace mulkin da sojoji suka yi shekaru 3 da suka wuce.

Mambobin majalisar dokokin wucin-gadi da sojoji suka kafa guda 71 ne suka amince da ƙudirin dokar, da aka gabatar.

A jawabin da ya gabatar wa al’ummar ƙasar ta kafar talabijin, ministan shari’a na ƙasar, Edasso Rodrigue Bayala ya ce duk wanda aka kama yana aikata neman maza zai gurfana a gaban alƙali, inda ya ƙara da cewa idan kuma ba dan ƙasa ba ne, za a tasa ƙeyarsa zuwa ƙasarsa.

Dokar na daga cikin dokokin da aka bijiro da su a ƙasar da zummar sake fasalin iyali da tsarin zamantakewar ‘yan ƙasa, kuma za a sanar da al’umma wannan doka ta wajen gudanar da gangami a faɗin ƙasar.

Mali, wadda aminiyar Burkina Faso ce, ta yi wannan doka  da ke haramta luwaɗi a watan Nuwamban shekarar 2024.

Ghana da Uganda sun tsaurara dokokinsu da ke yaƙi da ɗabi’ar neman maza a cikin shekarun baya-bayan nan, lamarin da ya janyo caccaka.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 200 Sun Mutu Sakomakon Girgizar ƙasar a ColombiaShahararren Mawaƙin Najeriya, Davido ya Rubuta wa Trump Wasiƙa Kan Zaɓen Jihar OsunHukumar NHRC ta Buƙaci a Kama Malamin Addinin, Sheikh JingirRundunar sojin Najeriya ta Daƙile Shirin Ƴan Bindiga a FilatoJami'an Ƴan Sanda 10 Sun Mutu Yayin Artabu da Ƴan Bindiga a Jihar KebbiAn Naɗa ɗan Najeriya Gidado Shuaib Wakilin Matasa na IPRA-UN Gabanin GWAEFCC da "Wuce Gona da Iri" da Tambayar 2027: Shin ana Rudar da Tinubu ta Hanyar Mutanen da ke Kewaye da Shi ? Daga Yushau A. ShuaibAn Samu Gawar Yara 3 da guda 1 a Sume a Gidan Mai Maganin GargajiyaMene ne Ainihin Abin da ya faru Aka Rufe Asusun Bankunan Gwamnatin Osun ?Jami'an Tsaro Sun Ceto Mutane 308 a Jihohin Arewacin Najeriya An Kama Mutane 6 da Ake Zargin da Taimaka wa Mayaƙan ISWAP a Jihar BornoZaɓen 2027: PDP ta Miƙa Sunan Jonathan ga INEC a Matsayin ɗan Takararta na Shugaban ƙasaIyanen Babban Jami'in Kula da Harkokin Kuɗaɗen ƙungiyar ISWAP Sun Miƙa Wuya ga SojojiAna Zargin Mayaƙan Boko Haram da Kashe Sojojin Nijar 14Gombe 2027: Malamai da Mambobin APC Sun yi Allah-wadai da Sukar Rarara ga Pantami
X whatsapp