Home General Kotu ta yanke wa kwamandan Ansaru hukunci ɗaurin shekaru 15

Kotu ta yanke wa kwamandan Ansaru hukunci ɗaurin shekaru 15

Court

Wata babba kotu a Abuja babban birnin Najeriya ta yanke wa Mahmud Usman, ɗaya daga cikin kwamandojin ƙungiyar Ansaru hukuncin ɗaurin shekaru 15 a gidan yari.

Mutumin wanda hukumar tsaro ta DSS ta gurfanar a ranar Alhamis ya amsa laifin gudanar da harkokin haƙar ma’adinai ba bisa ƙa’ida ba, lamarin da ya ba shi damar mallakar makamai da aikata ayyukan ta’addanci da garkuwa da mutane.

Alƙalin kotun mai shari’a Emeka Nwite, ya bayar da umarnin a ajiye Mahmud Usman a ofishin hukumar DSS har zuwa lokacin da za a kammal shari’a kan sauran zarge-zargen da ake masa guda 31.

A lokacin gabatar da ƙarar, an tuhumi Mahmud Usman da Abubakar Abba da aikata ta’addanci a 2022, ta hanyar kai hari kan barikin soji ta Wawa da ke Ka’inji a ƙaramar hukumar Borgu ta jihar Niger, lamain da ya yi sanadiyar kisan mutane da dama.

Ana zargin su da koyon horo a kan sarrafa makamai da haɗa bama-bamai a sansanonin ƴan ta’ada da dama.

Mai shari’a Nwite ya sanya ranar 21 ga watan Oktoba a matsayin ranar da za a ci gaba da shari’ar.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mayaƙan Lakurawa Sun Kashe Sojoji 7 a SokotoAn faɗa wa Shugaba Tinubu Cewa Ina Kitsa Yadda Zan Kashe Shi - ShettimaRundunar 'Yan Sandan Najeriya ta Ceto ƴan Mali 30 Daga Hannun Masu Safarar MutaneMun Kashe Mayaƙan ISIS 175 - Rundunar Sojin NajeriyaFarfesa Pantami ya Janye Daga Takarar Gwamnan Jihar GombeKishiya: Tsakanin ONSA na Ribadu da Tsaron Gida Famadewa Daga Yushau A. ShuaibZaben Fidda Gwani: An Harbe Mutum a Jihar PlateauRundunar 'Yan Sanda ta Tabbatar Kashe Jami'anta 17 a YobeSatar Kayayyakin Banki: An Kama Mutane Huɗu a Jihar Gombe'Yan Bindiga Sun Sace Basarake Tare da Mata 2 a KatsinaJami'an Kwastam Biyu sun Rasa Ransu a Fafatawa da LakurawaMatar Aure ta Zuba wa Kishiyarta da 'Ya'yanta Biyu Fetur Tare da Banka Musu Wuta a KanoIna da ƴancin Mu'amala da Kowa ba Tare da La'akari da Jam'iyya ba - WikeAdadin Masu Fama da Cutar Tamowa na ƙaruwa a Najeriya - MSFGwamnatin Yobe ta Sha Alwashin Kawo ƙarshen Hare-Haren Boko Haram
X whatsapp