Home Labarai Wata kotun Majistiri a Kano ta bawa Jami’an KAROTA umarni

Wata kotun Majistiri a Kano ta bawa Jami’an KAROTA umarni

Wata kotun tafi da gidanka a jihar Kano ta umarci jami’an hukumar dake lura da zirga-zirgar ababan hawa ta jihar Kano KAROTA da su kasance masu gudanar da ayyukansu cikin gaskiya da rikon Amana.

Mai shari’a Chief Majistire Halima Wali ce tayi umarnin yayin da take yanke hukunci kan wasu daga cikin mutane 82 da aka kama da laifukan karya dokokin hanya a jihar kano.

Wannan na cikin wata sanarwa da kakakin hukumar Abubakar Ibrahim Sharada Anipr ya fitar kuma aka raba manema labarai a jihar Kano.

Wadanda aka yankewa hukuncin sun an same su da laifin karya dokokin hanya da suka hadar da sabawa dokar fitilar bada hannu a manyan titunan kwayar birnin jihar.

Kotunan guda biyu da suka zauna a mahadar Kwanar Sabo da ke kan titin zuwa Maiduguri, da kuma Mahadar Mambayya dake gwammaja a jihar kano karkashin jagorancin Mai shari’a hauwa Abba da Mai Shari’a Halima Wali.

Da yake jawabi ga manema labarai Shugaban hukumar ta KAROTA Hon. Faisal Mahmud Kabir ya yabawa Alkalan kutunan bisa jajircewarsu da sadaukarwa da suke wajin tabbatar da an bi dokokin hukumar.

Haka kuma ya tabbatar da cewa hukumar zata samar da dukkan abinda ake bukata domin gudanar zaman kotunan Tafi da gidan ka yadda ya kamata

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mayaƙan Lakurawa Sun Kashe Sojoji 7 a SokotoAn faɗa wa Shugaba Tinubu Cewa Ina Kitsa Yadda Zan Kashe Shi - ShettimaRundunar 'Yan Sandan Najeriya ta Ceto ƴan Mali 30 Daga Hannun Masu Safarar MutaneMun Kashe Mayaƙan ISIS 175 - Rundunar Sojin NajeriyaFarfesa Pantami ya Janye Daga Takarar Gwamnan Jihar GombeKishiya: Tsakanin ONSA na Ribadu da Tsaron Gida Famadewa Daga Yushau A. ShuaibZaben Fidda Gwani: An Harbe Mutum a Jihar PlateauRundunar 'Yan Sanda ta Tabbatar Kashe Jami'anta 17 a YobeSatar Kayayyakin Banki: An Kama Mutane Huɗu a Jihar Gombe'Yan Bindiga Sun Sace Basarake Tare da Mata 2 a KatsinaJami'an Kwastam Biyu sun Rasa Ransu a Fafatawa da LakurawaMatar Aure ta Zuba wa Kishiyarta da 'Ya'yanta Biyu Fetur Tare da Banka Musu Wuta a KanoIna da ƴancin Mu'amala da Kowa ba Tare da La'akari da Jam'iyya ba - WikeAdadin Masu Fama da Cutar Tamowa na ƙaruwa a Najeriya - MSFGwamnatin Yobe ta Sha Alwashin Kawo ƙarshen Hare-Haren Boko Haram
X whatsapp