Home Labarai INEC: Majalisar Ƙoli ta Ƙasa ta Amince da Farfesa Joash Amupitan

INEC: Majalisar Ƙoli ta Ƙasa ta Amince da Farfesa Joash Amupitan

Amupitan

Majalisar Ƙoli ta Ƙasa ta amince da nadin Farfesa Joash Ojo Amupitan (SAN) daga jihar Kogi, dake yankin Arewacin Tsakiya, a matsayin sabon shugaban Hukumar Zaɓe mai zaman kanta ta Ƙasa (INEC).

Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu ne ya gabatar da sunansa domin maye gurbin Farfesa Mahmood Yakubu, wanda ya kammala wa’adinsa a watan Oktoba 2025 bayan shafe shekaru 10 a kujerar shugabancin hukumar. Shugaba Tinubu ya ce Amupitan shi ne ɗan jihar Kogi na farko da aka gabatar don wannan mukami, kuma mutum ne da aka sheda baya tsangwama irin ta siyasa.

Farfesa Amupitan, mai shekaru 58 daga Ayetoro Gbede, karamar hukumar Ijumu a jihar Kogi, malami ne a fannin shari’a a Jami’ar Jos, inda yake rike da mukamin Mataimakin Shugaban Jami’a (Harkokin Gudanarwa). Ya kware a fannoni da suka haɗa da Company Law, Law of Evidence, Corporate Governance da Privatisation Law. Ya zama Lauya Babban (SAN) a shekarar 2014.

Ya fara karatunsa a Kwara Polytechnic tsakanin 1982 da 1984 kafin ya ci gaba a Jami’ar Jos daga 1984 zuwa 1987. Ya kammala karatun sa na Shari’a a matakin farko a 1988, sannan ya kammala digirin LLM a 1993 da kuma PhD a 2007 a UNIJOS. Har ila yau, ya yi aikin yi wa ƙasa hidima a gidan jaridar jihar Bauchi tsakanin 1988 da 1989.

Baya ga karantarwa, Amupitan ya riƙe manyan mukamai a harkar gudanarwa da harkokin ilimi, ciki har da Shugaban Kwamitin Shugabannin Sassa da Daraktoci (2012-2014), Dekan na Faculty of Law (2008-2014), da Shugaban Sashen Public Law (2006-2008). A halin yanzu, shi ne Shugaban Majalisar Gudanarwa na Jami’ar Joseph Ayo Babalola da ke Osun.

Ya wallafa littattafai da dama a fannin shari’a, ciki har da Corporate Governance: Models and Principles (2008), Documentary Evidence in Nigeria (2008), Evidence Law: Theory and Practice in Nigeria (2013), da Principles of Company Law (2013).

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mayaƙan Lakurawa Sun Kashe Sojoji 7 a SokotoAn faɗa wa Shugaba Tinubu Cewa Ina Kitsa Yadda Zan Kashe Shi - ShettimaRundunar 'Yan Sandan Najeriya ta Ceto ƴan Mali 30 Daga Hannun Masu Safarar MutaneMun Kashe Mayaƙan ISIS 175 - Rundunar Sojin NajeriyaFarfesa Pantami ya Janye Daga Takarar Gwamnan Jihar GombeKishiya: Tsakanin ONSA na Ribadu da Tsaron Gida Famadewa Daga Yushau A. ShuaibZaben Fidda Gwani: An Harbe Mutum a Jihar PlateauRundunar 'Yan Sanda ta Tabbatar Kashe Jami'anta 17 a YobeSatar Kayayyakin Banki: An Kama Mutane Huɗu a Jihar Gombe'Yan Bindiga Sun Sace Basarake Tare da Mata 2 a KatsinaJami'an Kwastam Biyu sun Rasa Ransu a Fafatawa da LakurawaMatar Aure ta Zuba wa Kishiyarta da 'Ya'yanta Biyu Fetur Tare da Banka Musu Wuta a KanoIna da ƴancin Mu'amala da Kowa ba Tare da La'akari da Jam'iyya ba - WikeAdadin Masu Fama da Cutar Tamowa na ƙaruwa a Najeriya - MSFGwamnatin Yobe ta Sha Alwashin Kawo ƙarshen Hare-Haren Boko Haram
X whatsapp