Home Labarai Dalilin da ya sa Amnesty ke neman a soke hukuncin kisa a...

Dalilin da ya sa Amnesty ke neman a soke hukuncin kisa a Najeriya

Ƙungiyar kare haƙƙin bil’adama ta Amnesty International ta yi kira ga hukumomin Nijeriya da su soke hukuncin kisa a ƙasar.

Manajar shirye-shirye ta ƙungiyar, Mrs Barbara Magaji ce ta bayyana hakan a Abuja lokacin da take jawabi a taron masu ruwa da tsaki a Ranar Yaƙi da Hukuncin Kisa ta Duniya.

Ƙungiyar ce dai ta shira taron da haɗin gwiwar ofishin jakadancin Faransa a ƙasar.

Barbara Magaji ta buƙaci a cire dokokin da suka tanadi hukunce-hukuncen kisa daga kundin tsarin mulkin ƙasar da kuma dokokin wasu jihohin ƙasar.

Ta ce ya kamata majalisar dokokin ƙasar ta duba yiwuwar soke hukuncin kisa ga duka manyan laifukan da aka tanadar wa hukuncin a kundin tsarin mulkin ƙasar.

“Babu wata hujja da ke nuna cewa hukuncin kisa na rage aukuwar manyan laifukan”, in ji ta.

A yanzu haka dai jihohin ƙasar 26 da Abuja ne suke da dokokin da suka tanadin hukuncin kisa ga laifukan da suka shafi garkuwa da mutane da fashi da satar shanu da tsafi.

“Duk da tanadin hukuncin kisa a waɗannan jihohin, amma kullum ana ci gaba da samun ƙaruwar irin waɗannan laifukan, musamman garkuwa a mutane da fashi da ma sauran laifukan.”

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 200 Sun Mutu Sakomakon Girgizar ƙasar a ColombiaShahararren Mawaƙin Najeriya, Davido ya Rubuta wa Trump Wasiƙa Kan Zaɓen Jihar OsunHukumar NHRC ta Buƙaci a Kama Malamin Addinin, Sheikh JingirRundunar sojin Najeriya ta Daƙile Shirin Ƴan Bindiga a FilatoJami'an Ƴan Sanda 10 Sun Mutu Yayin Artabu da Ƴan Bindiga a Jihar KebbiAn Naɗa ɗan Najeriya Gidado Shuaib Wakilin Matasa na IPRA-UN Gabanin GWAEFCC da "Wuce Gona da Iri" da Tambayar 2027: Shin ana Rudar da Tinubu ta Hanyar Mutanen da ke Kewaye da Shi ? Daga Yushau A. ShuaibAn Samu Gawar Yara 3 da guda 1 a Sume a Gidan Mai Maganin GargajiyaMene ne Ainihin Abin da ya faru Aka Rufe Asusun Bankunan Gwamnatin Osun ?Jami'an Tsaro Sun Ceto Mutane 308 a Jihohin Arewacin Najeriya An Kama Mutane 6 da Ake Zargin da Taimaka wa Mayaƙan ISWAP a Jihar BornoZaɓen 2027: PDP ta Miƙa Sunan Jonathan ga INEC a Matsayin ɗan Takararta na Shugaban ƙasaIyanen Babban Jami'in Kula da Harkokin Kuɗaɗen ƙungiyar ISWAP Sun Miƙa Wuya ga SojojiAna Zargin Mayaƙan Boko Haram da Kashe Sojojin Nijar 14Gombe 2027: Malamai da Mambobin APC Sun yi Allah-wadai da Sukar Rarara ga Pantami
X whatsapp