Home Bincike Rikici tsakanin Boko Haram da ISWAP ya yi ajalin mayaƙa sama da

Rikici tsakanin Boko Haram da ISWAP ya yi ajalin mayaƙa sama da

Rahotanni daga yankin arewa maso gabashin Najeriya na nuna cewa rikicin cikin gida tsakanin ɓangaren Boko Haram da tsagin ISWAP ya yi sanadiyar mutuwar aƙalla mayaƙa guda 200 a tsakaninsu.

Kafar AFP ta ruwaito cewa ricikin ya yi ƙamari ne a tsakanin ɓangarorin ƙungiyar guda biyu a yankin Dogon Chiku da ke gaɓar Tekun Chadi a ranar Lahadi, wanda ya kasance ɗaya daga rigingimu da ya fi zafi saboda bambancin ra’ayi.

“Mun ƙirga aƙalla gawarwaki guda 200,” in ji wani mai suna Babakura Kolo a zantawarsa a AFP.

Wani tubabben ɗan Boko Haram da ke bibiyar harkokinsu da ya ce a kira shi da suna Saddiku ma ya tabbatar da rikicin, inda ya ce, “an kashe aƙalla ƴan ISWAP 200 a rigimar, sannan an kwashe muku makamai da dama, sannan aka kashe ƴan tsagin Boko Haram guda huɗu.”

Ya ƙara da cewa wannan ne rigima mafi zafi da aka yi a tsakanin ɓangarorin mayaƙan guda biyu tun bayan rabewarsu saboda saɓanin fahimta a shekarar 2016.

Wata majiyar tsaro ma ta tabbatar da aukuwar rigimar, inda ta ce “muna da bayanan sirri kan rigimar, kuma mun samu labarin mutuwar mayaƙa sama da 150, wanda kuma labari ne mai kyau a wajenmu.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 200 Sun Mutu Sakomakon Girgizar ƙasar a ColombiaShahararren Mawaƙin Najeriya, Davido ya Rubuta wa Trump Wasiƙa Kan Zaɓen Jihar OsunHukumar NHRC ta Buƙaci a Kama Malamin Addinin, Sheikh JingirRundunar sojin Najeriya ta Daƙile Shirin Ƴan Bindiga a FilatoJami'an Ƴan Sanda 10 Sun Mutu Yayin Artabu da Ƴan Bindiga a Jihar KebbiAn Naɗa ɗan Najeriya Gidado Shuaib Wakilin Matasa na IPRA-UN Gabanin GWAEFCC da "Wuce Gona da Iri" da Tambayar 2027: Shin ana Rudar da Tinubu ta Hanyar Mutanen da ke Kewaye da Shi ? Daga Yushau A. ShuaibAn Samu Gawar Yara 3 da guda 1 a Sume a Gidan Mai Maganin GargajiyaMene ne Ainihin Abin da ya faru Aka Rufe Asusun Bankunan Gwamnatin Osun ?Jami'an Tsaro Sun Ceto Mutane 308 a Jihohin Arewacin Najeriya An Kama Mutane 6 da Ake Zargin da Taimaka wa Mayaƙan ISWAP a Jihar BornoZaɓen 2027: PDP ta Miƙa Sunan Jonathan ga INEC a Matsayin ɗan Takararta na Shugaban ƙasaIyanen Babban Jami'in Kula da Harkokin Kuɗaɗen ƙungiyar ISWAP Sun Miƙa Wuya ga SojojiAna Zargin Mayaƙan Boko Haram da Kashe Sojojin Nijar 14Gombe 2027: Malamai da Mambobin APC Sun yi Allah-wadai da Sukar Rarara ga Pantami
X whatsapp