Home Labarai SERAP ta buƙaci CBN ya dawo da Naira triliyan 3 da ake...

SERAP ta buƙaci CBN ya dawo da Naira triliyan 3 da ake zargin sun yi ɓatan dabo

Ƙungiyar Kare Haƙƙin Jama’a da Kula da Al’amuran Tattalin Arziki (SERAP), ta bai wa Gwamnan Babban Bankin Najeriya (CBN), Olayemi Cardoso, kwanaki bakwai da ya fitar da bayanai kan Naira Tiriliyan 3 na kuɗaɗen al’umma da ake zargin sun yi batan dabo.

Ƙungiyar ta bayyana cewa wannan lamari na zuwa ne bayan wani rahoton Babban Ma’ajin Kasa na shekara ta 2022, wanda ya buƙaci CBN ya bayyana inda kuɗaɗen suka shiga.

Rahoton ya nuna akwai matsalar ɓacewar rarar kudi da basukan da ba a biya ba da kuma kwangiloli masu cike da ayoyin tambaya.

SERAP ta ce CBN ya gaza tura sama da naira triliyan 1 da biliyan 440 na rarar kudi na gwamnatin tarayya zuwa asusun kuɗaɗen shiga na bai ɗaya.

A sanarwar da ta fitar, SERAP ta lura cewa CBN bai karɓo sama da naira biliyan 700 ba na basussukan da kuɗaden kai dauki da aka bayar tsakanin 2018 zuwa Mayun 2022 ba.

Haka kuma CBN ya bayar da kwangiloli 43, na sama da Naira biliyan 189, sai dai ƴan kwangilar sun yi jinkiri da gangan inda daga baya suka buƙaci a sauya farashin kwangilar wanda ya kai ga biyan kuɗi fiye da Naira biliyan 9 ba bisa ƙa’ida ba.

Tana kuma fargabar za a iya karkatar da waɗannan kudaɗen don haka ne ta nemi a gaggauta dawo da su baitul malin gwamnati, ko ta ɗauki matakin shari’ah.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mayaƙan Lakurawa Sun Kashe Sojoji 7 a SokotoAn faɗa wa Shugaba Tinubu Cewa Ina Kitsa Yadda Zan Kashe Shi - ShettimaRundunar 'Yan Sandan Najeriya ta Ceto ƴan Mali 30 Daga Hannun Masu Safarar MutaneMun Kashe Mayaƙan ISIS 175 - Rundunar Sojin NajeriyaFarfesa Pantami ya Janye Daga Takarar Gwamnan Jihar GombeKishiya: Tsakanin ONSA na Ribadu da Tsaron Gida Famadewa Daga Yushau A. ShuaibZaben Fidda Gwani: An Harbe Mutum a Jihar PlateauRundunar 'Yan Sanda ta Tabbatar Kashe Jami'anta 17 a YobeSatar Kayayyakin Banki: An Kama Mutane Huɗu a Jihar Gombe'Yan Bindiga Sun Sace Basarake Tare da Mata 2 a KatsinaJami'an Kwastam Biyu sun Rasa Ransu a Fafatawa da LakurawaMatar Aure ta Zuba wa Kishiyarta da 'Ya'yanta Biyu Fetur Tare da Banka Musu Wuta a KanoIna da ƴancin Mu'amala da Kowa ba Tare da La'akari da Jam'iyya ba - WikeAdadin Masu Fama da Cutar Tamowa na ƙaruwa a Najeriya - MSFGwamnatin Yobe ta Sha Alwashin Kawo ƙarshen Hare-Haren Boko Haram
X whatsapp