Home AFIRKA ECOWAS ta dakatar da Guinea Bissau sakamakon juyin mulkin Sojoji

ECOWAS ta dakatar da Guinea Bissau sakamakon juyin mulkin Sojoji

Ƙungiyar ECOWAS ta dakatar da Guinea-Bissau kwanaki biyu bayan juyin mulkin da ya kawo ƙarshen gwamnatin shugaba Umaro Sissoco Embalo daidai lokacin da ake dakon sakamakon zaɓen da shugaban ke neman tazarce.

ECOWAS ta bayyana juyin mulkin na Guinea Bissau a matsayin babbar barazana ga tsarin dimokaraɗiyya a ƙasar ta yammacin Afrika.

Cikin matsayar da wannan taro na ECOWAS ya cimma, akwai dakatar da wannan ƙungiyar da kuma matsa mata lamba don ganin ta koma mulkin farar hula don tabbatar da demokraɗiyya.

Tuni dai hamɓararren shugaban na Guinea Bissau, Umaro Sissoco Embalo ya sauka a ƙasar Senegal a wani jirgi na musamman jiya Alhamis, biyo bayan shiga tsakani da ƙungiyar ECOWAS ta yi, kamar yadda ma’aikatar harkokin wajen Senegal ta bayyana.

Wannan ne juyin mulki na 9 da ake fuskanta a ƙasashen yammaci da Tsakiyar Afirka cikin shekaru biyar da suka gabata.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 200 Sun Mutu Sakomakon Girgizar ƙasar a ColombiaShahararren Mawaƙin Najeriya, Davido ya Rubuta wa Trump Wasiƙa Kan Zaɓen Jihar OsunHukumar NHRC ta Buƙaci a Kama Malamin Addinin, Sheikh JingirRundunar sojin Najeriya ta Daƙile Shirin Ƴan Bindiga a FilatoJami'an Ƴan Sanda 10 Sun Mutu Yayin Artabu da Ƴan Bindiga a Jihar KebbiAn Naɗa ɗan Najeriya Gidado Shuaib Wakilin Matasa na IPRA-UN Gabanin GWAEFCC da "Wuce Gona da Iri" da Tambayar 2027: Shin ana Rudar da Tinubu ta Hanyar Mutanen da ke Kewaye da Shi ? Daga Yushau A. ShuaibAn Samu Gawar Yara 3 da guda 1 a Sume a Gidan Mai Maganin GargajiyaMene ne Ainihin Abin da ya faru Aka Rufe Asusun Bankunan Gwamnatin Osun ?Jami'an Tsaro Sun Ceto Mutane 308 a Jihohin Arewacin Najeriya An Kama Mutane 6 da Ake Zargin da Taimaka wa Mayaƙan ISWAP a Jihar BornoZaɓen 2027: PDP ta Miƙa Sunan Jonathan ga INEC a Matsayin ɗan Takararta na Shugaban ƙasaIyanen Babban Jami'in Kula da Harkokin Kuɗaɗen ƙungiyar ISWAP Sun Miƙa Wuya ga SojojiAna Zargin Mayaƙan Boko Haram da Kashe Sojojin Nijar 14Gombe 2027: Malamai da Mambobin APC Sun yi Allah-wadai da Sukar Rarara ga Pantami
X whatsapp