Home AFIRKA ECOWAS ta dakatar da Guinea Bissau sakamakon juyin mulkin Sojoji

ECOWAS ta dakatar da Guinea Bissau sakamakon juyin mulkin Sojoji

Ƙungiyar ECOWAS ta dakatar da Guinea-Bissau kwanaki biyu bayan juyin mulkin da ya kawo ƙarshen gwamnatin shugaba Umaro Sissoco Embalo daidai lokacin da ake dakon sakamakon zaɓen da shugaban ke neman tazarce.

ECOWAS ta bayyana juyin mulkin na Guinea Bissau a matsayin babbar barazana ga tsarin dimokaraɗiyya a ƙasar ta yammacin Afrika.

Cikin matsayar da wannan taro na ECOWAS ya cimma, akwai dakatar da wannan ƙungiyar da kuma matsa mata lamba don ganin ta koma mulkin farar hula don tabbatar da demokraɗiyya.

Tuni dai hamɓararren shugaban na Guinea Bissau, Umaro Sissoco Embalo ya sauka a ƙasar Senegal a wani jirgi na musamman jiya Alhamis, biyo bayan shiga tsakani da ƙungiyar ECOWAS ta yi, kamar yadda ma’aikatar harkokin wajen Senegal ta bayyana.

Wannan ne juyin mulki na 9 da ake fuskanta a ƙasashen yammaci da Tsakiyar Afirka cikin shekaru biyar da suka gabata.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mayaƙan Lakurawa Sun Kashe Sojoji 7 a SokotoAn faɗa wa Shugaba Tinubu Cewa Ina Kitsa Yadda Zan Kashe Shi - ShettimaRundunar 'Yan Sandan Najeriya ta Ceto ƴan Mali 30 Daga Hannun Masu Safarar MutaneMun Kashe Mayaƙan ISIS 175 - Rundunar Sojin NajeriyaFarfesa Pantami ya Janye Daga Takarar Gwamnan Jihar GombeKishiya: Tsakanin ONSA na Ribadu da Tsaron Gida Famadewa Daga Yushau A. ShuaibZaben Fidda Gwani: An Harbe Mutum a Jihar PlateauRundunar 'Yan Sanda ta Tabbatar Kashe Jami'anta 17 a YobeSatar Kayayyakin Banki: An Kama Mutane Huɗu a Jihar Gombe'Yan Bindiga Sun Sace Basarake Tare da Mata 2 a KatsinaJami'an Kwastam Biyu sun Rasa Ransu a Fafatawa da LakurawaMatar Aure ta Zuba wa Kishiyarta da 'Ya'yanta Biyu Fetur Tare da Banka Musu Wuta a KanoIna da ƴancin Mu'amala da Kowa ba Tare da La'akari da Jam'iyya ba - WikeAdadin Masu Fama da Cutar Tamowa na ƙaruwa a Najeriya - MSFGwamnatin Yobe ta Sha Alwashin Kawo ƙarshen Hare-Haren Boko Haram
X whatsapp