Home Labarai Wadanda aka sace a Cocin jihar Kwara sun shaki iskar ‘yanci

Wadanda aka sace a Cocin jihar Kwara sun shaki iskar ‘yanci

Rahotanni na bayyana cewa masu bauta 38 da aka sace a cocin Kwara da ke ƙaramar hukumar Eruku a ranar 18 ga Nuwamba, 2025, harin da ya yi sanadiyyar mutuwar mutum uku tare da jikkatar wani sun koma gida lafiya bayan an kubutar da su.

A wata sanarwa da mai magana da yawun shugaban ƙaramar hukumar Ekiti, Dada Sunday ya fitar a daren Talata, ya tabbatar da cewa gwamnan jihar, AbdulRahman AbdulRazaq ne ya miƙa waɗanda aka ceto ga shugaban ƙaramar hukumar Ekiti, Honourable Awelewa Olawale Gabriel, a birnin Ilorin.

Da yake karɓar wadanda aka ceto, Awelewa ya bayyana godiyarsa ga shugaban ƙasa Bola Ahmed Tinubu da gwamna AbdulRazaq da duka hukumomin tsaro bisa gaggawa da ƙoƙari wajen ceton mutanen.

Ya ce aikin haɗin gwiwar jami’an tsaro da gwamnati ya taimaka wajen kammala ceto cikin lokaci, tare da ba wa wanɗanda aka kuutar cikakkiyar kulawa.

Sanarwar ta ce tawagar waɗanda aka ceto ta isa garin Eruku da misalin ƙarfe 6:30 na yammacin Talata, inda dangi da mazauna yankin suka tarbe su cikin murna da farin ciki.

Shugaban ƙaramar hukumar ya tabbatar wa mazauna yankin cewa gwamnati za ta ci gaba da bai wa tsaro mahimmanci, tare da ƙarfafa matakan kare rayuka da dukiyoyi a dukkan gundumomi 10 na yankin.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp