Home Labarai Majalisa ta amince da naɗin Chris Musa ministan tsaron Najeriya

Majalisa ta amince da naɗin Chris Musa ministan tsaron Najeriya

Majalisar Dattawan Najeriya ta amince da naɗin Janar Christopher Musa a matsayin sabon ministan tsaro.

Zaman majalisar ya cika da ruɗani a yau Laraba yayin da wasu ‘yanmajalisar ke cewa janar ɗin, wanda shi ne tsohon babban hafsan tsaron Najeriya, ya rusuna ya wuce ba tare da amsa tambayoyi masu yawa ba, da kuma waɗanda suka ce dole sai ya amsa.

Daga ƙarshe dai Shugaban Majalisa Godswill Akpabio ya shawo kan hayaniyar kuma ya amince cewa akwai buƙatar Janar Musa mai ritaya ya amsa tambayoyin da suka dace.

Da yake jawabi, janar ɗin ya bayyana shirinsa na shawo kan matsalar tsaro, da kuma dawo da martabar rundunar sojin ƙasar a idon ‘yan Najeriya.

“Wannan ba lokaci ne na yin siyasar “rusuna ka wuce ba”. Hatta Donald Trump yana matsa mana. Ba game-garin mutum ba ne, tsohon babban hafsan tsaro ne,” kamar yadda Akpabio ya bayyana lokacin da ya miƙe daga kujerarsa lokacin da ake hayaniyar.

Ana sa ran Janar Musa zai fara aiki nan take bayan Mohammed Badaru ya sauka daga muƙamin a ranar Litinin.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp