Home Labarai Gwamnatin Nijeriya ta yi watsi da kudirin hukuncin kisa ga masu garkuwa

Gwamnatin Nijeriya ta yi watsi da kudirin hukuncin kisa ga masu garkuwa

Gwamnatin Najeriya ta bayyana cewa ba ta goyon bayan ƙudirin majalisar dattawa na gyara dokar yaƙi da ta’addanci wadda ta ce a riƙa yanke wa masu sace mutane hukuncin kisa.

Wannan na zuwa ne bayan lauyan gwamnati kuma ministan Shari’a na ƙasar, Lateef Fagbemi ya ce bai kamata a riƙa yanke wa masu garkuwa da mutane hukuncin kisa ba.

Fagbemi ya nuna damuwa kan yiwuwar cewa ƙasashen duniya za su iya ƙin miƙa wa Najeriya masu laifi bisa dogaro da kauce wa hukuncin kisa da kuma dalilan jin ƙan ɗan’adam.

Ya ce, “Dole ne mu yi la’akari da matsalolin da ke tattare da sanya hukuncin kisa a cikin doka, musamman yadda hakan zai iya kawo cikas ga haɗin gwiwar ƙasashen duniya wajen yaƙi da ta’addanci.”

“Yawancin ƙasashe abokan hulɗarmu za su iya ƙin mika wa Najeriya manyan masu laifi idan suna fuskantar barazanar hukuncin kisa.”

Ministan ya kara da cewa, “Ta hanyar saka wannan hukunci, zai iya samar da mafaka ga manyan masu laifi a ƙasashen waje, domin kotunan ƙasashen waje za su hana a mayar da su Najeriya bisa dalilan kare hakkokin ɗan’adam.”

Ƙudirin dai ya ƙunshi yanke wa masu garkuwa da mutane hukuncin kisa ba tare da yiwuwar sassaucin kotu ko tara ba, inda aka fara karantawa a majalisar a ranar 27 ga watan Nuwamba, sai na biyu kuma a ranar 3 ga watan Disamba.

Fagbemi ya bayyana waɗannan hujjoji ne a lokacin taron jin ra’ayin jama’a da majalisar ta shirya tare da haɗin gwiwar kwamitocin haƙƙokin ɗan’adam da Shari’a da tsaro da tattara bayanan sirri, da ma’aikatar cikin gida.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 200 Sun Mutu Sakomakon Girgizar ƙasar a ColombiaShahararren Mawaƙin Najeriya, Davido ya Rubuta wa Trump Wasiƙa Kan Zaɓen Jihar OsunHukumar NHRC ta Buƙaci a Kama Malamin Addinin, Sheikh JingirRundunar sojin Najeriya ta Daƙile Shirin Ƴan Bindiga a FilatoJami'an Ƴan Sanda 10 Sun Mutu Yayin Artabu da Ƴan Bindiga a Jihar KebbiAn Naɗa ɗan Najeriya Gidado Shuaib Wakilin Matasa na IPRA-UN Gabanin GWAEFCC da "Wuce Gona da Iri" da Tambayar 2027: Shin ana Rudar da Tinubu ta Hanyar Mutanen da ke Kewaye da Shi ? Daga Yushau A. ShuaibAn Samu Gawar Yara 3 da guda 1 a Sume a Gidan Mai Maganin GargajiyaMene ne Ainihin Abin da ya faru Aka Rufe Asusun Bankunan Gwamnatin Osun ?Jami'an Tsaro Sun Ceto Mutane 308 a Jihohin Arewacin Najeriya An Kama Mutane 6 da Ake Zargin da Taimaka wa Mayaƙan ISWAP a Jihar BornoZaɓen 2027: PDP ta Miƙa Sunan Jonathan ga INEC a Matsayin ɗan Takararta na Shugaban ƙasaIyanen Babban Jami'in Kula da Harkokin Kuɗaɗen ƙungiyar ISWAP Sun Miƙa Wuya ga SojojiAna Zargin Mayaƙan Boko Haram da Kashe Sojojin Nijar 14Gombe 2027: Malamai da Mambobin APC Sun yi Allah-wadai da Sukar Rarara ga Pantami
X whatsapp