Home Labarai Ku daina kirana da na janye takarar shugabancin kasa a shekarar 2027

Ku daina kirana da na janye takarar shugabancin kasa a shekarar 2027

Tsohon Mataimakin shugaban ƙasa, Atiku Abubakar, ya yi gargaɗi kan kiraye-kirayen da ake yi masa na ya ajiye takara a yaƙin neman shugabancin kasa ƙarkashin jam’iyyar haɗaka ta ADC, yana mai cewa hakan cin amanar ‘yan Najeriya ne.

Sanarwar da mai bai wa Atiku shawara kan harkokin yaɗa labarai, Paul Ibe, ya fitar ta bayyana cewa duk wani yunkuri na ganin Atiku ya ajiye takara zai goyi bayan manufofin kama-karya ne kawai tare kuma da tauye hakkin dimokuradiyya a Najeriya.

Sanarwar ta ce a cikin shekaru kusan uku da suka gabata, ‘yan Najeriya sun fuskanci wahalhalu masu tsanani sakamakon manufofin tattalin arziƙi a ƙarkashin mulkin shugaba Bola Ahmed Tinubu.

Sanarwar ta kuma zargi gwamnatin Tinubu da ƙoƙarin mayar da siyasar Najeriya ta zama ƙarƙashin jam’iyya ɗaya ta hanyar raunana jam’iyyun adawa.

Sanarwar ta kara da cewa “Jam’iyyar ADC za ta ci gaba da gudanar da tsarin tsayar da ɗan takararta kuma duk wani matsin lamba daga APC ko masu tsoma baki daga waje ba zai yi tasiri ba saboda ba su da ikon yin zagon ƙasa kan wanda ADC za ta tsayar a matsayin ɗan takarar shugaban ƙasa.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Dangote ya ƙara farashin man feturHukumar Jin dadin alhazan Kano ta sanar da ranar fara jigilar maniyatantaYadda Lakurawa suka kashe masallata a KebbiDSS ta kama jagoran ISWAP da ake nema ruwa a jallo a EdoBa mu taɓa goyon bayan musguna wa Kristoci ba - Gwamnatin NajeriyaGobara ta tashi a babban kasuwar Fika da ke jihar YobeWaye Tunji Disu: Sabon Babban Sifeton 'Yansandan NajeriyaNijar ta amince da kundin ayyukan AES na shekara ta biyuAtiku ya zargi gwamnatin Tinubu da yi wa dimokuraɗiyya zagon ƙasaGwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanci
X whatsapp