Home Labarai Ƴansanda sun ɗauke makeken bam ɗin da aka gani a jihar Neja

Ƴansanda sun ɗauke makeken bam ɗin da aka gani a jihar Neja

Rundunar ƴansandan Najeriya a jihar Neja ta kwance tare da ɗauke wani makeken bam da aka gani a dajin Zugurma da ke karamar hukumar Mashegu.

A wata tattaunawa da BBC, shugaban ƙaramar hukumar Mashegu, Umar Igade ya ce bayan samun kiran waya daga ƙauyen Zugurma, cewa an ga wani abu kamar bam a ƙasa “na kira DPO na wannan yanki, inda ya tura jami’an tsaro domin su duba gaskiyar al’amarin.

“Bayan da suka isa wurin sun tabbatar da cewa bam ne. Bam ne mai girma, guda ɗaya.”

A baya-bayan nan an samu rahotanni daga wasu ƙauyuka a arewacin Najeriya kan yadda al’umma suke tsintar abubuwan fashewa, bayan wani hari da Amurka ta kai a ƙarshen watan Disamba kan wani yanki mai fama da ayyukan ƙungiyoyin masu ɗauke da makami.

Sai dai shugaban ƙaramar hukumar ya ce ya zuwa yanzu ba su da tabbas kan ko wannan bam da aka tsinta na daga cikin waɗanda Amurka ta yi amfani da su wajen kai harin na ranar 25 ga watan Disamba.

Ya ce “jami’an tsaro sun dauki bam din kuma suna kan bincike, saboda haka su ne za su tabbatar mana ko irin bam din da aka gani ne a Sokoto da Kwara waɗanda Amurka ta yi amfani da su wajen kai hari.”

“Masu warware bam sun zo daga Minna, sun kwance shi sun saka shi a mota kuma sun tafi da shi zuwa babban ofishin ƴansanda da ke garin Minna domin ci gaba da bincike,” a cewar Igade.

Neja na daga cikin jihohin Najeriya da ke fama da ayyukan ƴan bindiga wadanda ke kai hare-hare kan ƙauyuka suna kashewa da garkuwa da mutane domin karɓar kudin fansa.

A cikin ƙarshen makon da ya gabata ne wasu ƴan bindiga suka kai hari a ƙauyen Kasuwan Daji da ke jihar ta Neja inda ake zargin sun kashe mutum sama da 40.

Kuma a cikin watannin da suka gabata ƴan bindiga sun kai hari kan ƙauyen Papiri, inda suka yi garkuwa da sama da mutane 200, waɗanda suka hada da ɗalibai da malamai, waɗanda daga baya aka sako su.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 200 Sun Mutu Sakomakon Girgizar ƙasar a ColombiaShahararren Mawaƙin Najeriya, Davido ya Rubuta wa Trump Wasiƙa Kan Zaɓen Jihar OsunHukumar NHRC ta Buƙaci a Kama Malamin Addinin, Sheikh JingirRundunar sojin Najeriya ta Daƙile Shirin Ƴan Bindiga a FilatoJami'an Ƴan Sanda 10 Sun Mutu Yayin Artabu da Ƴan Bindiga a Jihar KebbiAn Naɗa ɗan Najeriya Gidado Shuaib Wakilin Matasa na IPRA-UN Gabanin GWAEFCC da "Wuce Gona da Iri" da Tambayar 2027: Shin ana Rudar da Tinubu ta Hanyar Mutanen da ke Kewaye da Shi ? Daga Yushau A. ShuaibAn Samu Gawar Yara 3 da guda 1 a Sume a Gidan Mai Maganin GargajiyaMene ne Ainihin Abin da ya faru Aka Rufe Asusun Bankunan Gwamnatin Osun ?Jami'an Tsaro Sun Ceto Mutane 308 a Jihohin Arewacin Najeriya An Kama Mutane 6 da Ake Zargin da Taimaka wa Mayaƙan ISWAP a Jihar BornoZaɓen 2027: PDP ta Miƙa Sunan Jonathan ga INEC a Matsayin ɗan Takararta na Shugaban ƙasaIyanen Babban Jami'in Kula da Harkokin Kuɗaɗen ƙungiyar ISWAP Sun Miƙa Wuya ga SojojiAna Zargin Mayaƙan Boko Haram da Kashe Sojojin Nijar 14Gombe 2027: Malamai da Mambobin APC Sun yi Allah-wadai da Sukar Rarara ga Pantami
X whatsapp