Home Labarai Sojojin sun gano makeken kabarin ƴan Boko Haram a yankin Timbuktu

Sojojin sun gano makeken kabarin ƴan Boko Haram a yankin Timbuktu

Rundunar sojin Najeriya ta bayyana cewa sojojin haɗin gwiwarta na Operation Haɗin kai da JTF sun gano wani makeken kabarin wasu mayaƙan Boko Haram a yankin Timbuktu, wanda aka ƙiyasta yana ɗauke da gawarwaki guda 20 da aka kashe.

Sanarwar rundunar ta ce wannan kabarin an gano shi ne yayin da sojoji ke ci gaba da ayyukan samame da ragargazar ‘yanbindiga a yankin, musamman a wani tashar jiragen ruwa da ke kilomita 6 arewa da Chilaria.

A yayin samamen, sojojin sun gamu da motoci biyu masu ɗauke da abubuwan fashewa.

Duk da cewa sun samu nasarar kawar da ɗaya daga cikin motocin, ɗayan motar ta fashe, lamarin da ya yi sanadiyyar mutuwar wasu daga cikin sojojin da kuma raunata wasu.

An gaggauta ɗaukar waɗanda suka ji rauni zuwa asibiti domin samun kulawa, yayin da rundunar ke ci gaba da ayyukanta na tabbatar da tsaro a yankin.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 200 Sun Mutu Sakomakon Girgizar ƙasar a ColombiaShahararren Mawaƙin Najeriya, Davido ya Rubuta wa Trump Wasiƙa Kan Zaɓen Jihar OsunHukumar NHRC ta Buƙaci a Kama Malamin Addinin, Sheikh JingirRundunar sojin Najeriya ta Daƙile Shirin Ƴan Bindiga a FilatoJami'an Ƴan Sanda 10 Sun Mutu Yayin Artabu da Ƴan Bindiga a Jihar KebbiAn Naɗa ɗan Najeriya Gidado Shuaib Wakilin Matasa na IPRA-UN Gabanin GWAEFCC da "Wuce Gona da Iri" da Tambayar 2027: Shin ana Rudar da Tinubu ta Hanyar Mutanen da ke Kewaye da Shi ? Daga Yushau A. ShuaibAn Samu Gawar Yara 3 da guda 1 a Sume a Gidan Mai Maganin GargajiyaMene ne Ainihin Abin da ya faru Aka Rufe Asusun Bankunan Gwamnatin Osun ?Jami'an Tsaro Sun Ceto Mutane 308 a Jihohin Arewacin Najeriya An Kama Mutane 6 da Ake Zargin da Taimaka wa Mayaƙan ISWAP a Jihar BornoZaɓen 2027: PDP ta Miƙa Sunan Jonathan ga INEC a Matsayin ɗan Takararta na Shugaban ƙasaIyanen Babban Jami'in Kula da Harkokin Kuɗaɗen ƙungiyar ISWAP Sun Miƙa Wuya ga SojojiAna Zargin Mayaƙan Boko Haram da Kashe Sojojin Nijar 14Gombe 2027: Malamai da Mambobin APC Sun yi Allah-wadai da Sukar Rarara ga Pantami
X whatsapp