Home Labarai Farfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCON

Farfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCON

Tsoho shugaban hukumar kula da aikin Hajji ta Ƙasa (NAHCON), Farfesa Sheikh Abdullah Saleh Usman, ya bayyana dalilan da suka sanya shi ya ajiye aiki a matsayin shugaban hukumar, wanda ya fara aiki daga ranar Litinin, 9 ga Fabrairu, 2026.

A wata sanarwa da ya fitar wadda da ya sanyawa hannu da kansa, Farfesa Abdullahi Saleh Usman ya bayyana cewa murabus ɗin nasa ya biyo bayan dalilai na kansa, bayan yin dogon tunani, addu’a da shawarwari da iyalansa.

Ya jaddada cewa matakin nasa ba shi da alaƙa da wata matsala ko rashin jituwa da Gwamnatin Tarayya ko hukumar NAHCON.

Tsohon shugaban NAHCON ya tabbatar da cewa ya miƙa takardar murabus ɗinsa a rubuce ga Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu, kamar yadda Sashe na 3(6) na Dokar Kafa Hukumar NAHCON ta shekarar 2006 ya tanada.

Farfesa Abdullahi Saleh Usman ya nuna godiya ga Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu bisa amincewa da damar da ya ba shi na yi wa ƙasa da al’ummar Musulmi hidima, tare da yabawa Mataimakin Shugaban Ƙasa Kashim Shettima kan shawarwari da goyon bayan da ya ba shi.

Haka kuma, ya miƙa godiya ga Mambobin Kwamitin Gudanarwa, ma’aikata da shugabannin sassan hukumar, yana mai yaba jajircewa da sadaukarwarsu wajen inganta aikin Hajjin Najeriya.

Ya kuma gode wa Hukumomin Jin Daɗin Alhazai na Jihohi, Kamfanonin Hajji, Kamfanonin Jiragen Sama da hukumomin Saudiyya bisa kyakkyawan haɗin gwiwa.

A ƙarshe, Farfesa Abdullahi Saleh Usman ya yi addu’ar Allah Ya karɓi ayyukan da aka gudanar, Ya jagoranci sabon shugabancin NAHCON, tare da roƙon Allah ya sa alhazan Najeriya su yi Hajji karɓaɓɓe (Hajj Mabrur)

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 200 Sun Mutu Sakomakon Girgizar ƙasar a ColombiaShahararren Mawaƙin Najeriya, Davido ya Rubuta wa Trump Wasiƙa Kan Zaɓen Jihar OsunHukumar NHRC ta Buƙaci a Kama Malamin Addinin, Sheikh JingirRundunar sojin Najeriya ta Daƙile Shirin Ƴan Bindiga a FilatoJami'an Ƴan Sanda 10 Sun Mutu Yayin Artabu da Ƴan Bindiga a Jihar KebbiAn Naɗa ɗan Najeriya Gidado Shuaib Wakilin Matasa na IPRA-UN Gabanin GWAEFCC da "Wuce Gona da Iri" da Tambayar 2027: Shin ana Rudar da Tinubu ta Hanyar Mutanen da ke Kewaye da Shi ? Daga Yushau A. ShuaibAn Samu Gawar Yara 3 da guda 1 a Sume a Gidan Mai Maganin GargajiyaMene ne Ainihin Abin da ya faru Aka Rufe Asusun Bankunan Gwamnatin Osun ?Jami'an Tsaro Sun Ceto Mutane 308 a Jihohin Arewacin Najeriya An Kama Mutane 6 da Ake Zargin da Taimaka wa Mayaƙan ISWAP a Jihar BornoZaɓen 2027: PDP ta Miƙa Sunan Jonathan ga INEC a Matsayin ɗan Takararta na Shugaban ƙasaIyanen Babban Jami'in Kula da Harkokin Kuɗaɗen ƙungiyar ISWAP Sun Miƙa Wuya ga SojojiAna Zargin Mayaƙan Boko Haram da Kashe Sojojin Nijar 14Gombe 2027: Malamai da Mambobin APC Sun yi Allah-wadai da Sukar Rarara ga Pantami
X whatsapp