Wata mummunar gobara ta tashi a babban kasuwar Fika da ke jihar Yobe inda ta ƙone wani ɓangare na kasuwar da ke arewa maso yammacin Najeriya.
Gobarar ta lalata rumfuna a kasuwar wadda ke hada-hada mako-mako, lamarin da ya jefa, ɗimbin mutanen da suka dogara da kasuwar wajen harkokin rayuwarsu cikin mawuyacin hali.
Gobarar dai ta tashi ne jiya da yamma daf da lokacin buɗa bakin azumin ramadan, inda ta mamaye rumfuna 135 wadanda aƙasarinsu na kwano da katako ne wasu kuma na itace da kara.
Shugaban hukumar bayar da agajin gaggawa ta jihar Yobe, Dr. Muhammad Goje ya tabbatar da aukuwar wannan gobara.
Ya ƙara da cewa gobarar ba ta shiga shaguna ba kuma ba a rasa rai ko ɗaya ,a a gobarar.
Dr Muhammad Goje ya ƙara da cewa wannan tashin gobara a kasuwar Fika itace ta uku da aka samu a kasuwanni daban-daban cikin kasa da wata daya a jihar ciki harda kasuwar Bukarti, inda rumfuna kusan dari suka ƙone, sai kuma kasuwar Fuchimiran a ƙaramar hukumar Geidam, inda rufunan da gidajen mutane da dama suka kone.










