Home General Gobara ta tashi a babban kasuwar Fika da ke jihar Yobe

Gobara ta tashi a babban kasuwar Fika da ke jihar Yobe

Wata mummunar gobara ta tashi a babban kasuwar Fika da ke jihar Yobe inda ta ƙone wani ɓangare na kasuwar da ke arewa maso yammacin Najeriya.

Gobarar ta lalata rumfuna a kasuwar wadda ke hada-hada mako-mako, lamarin da ya jefa, ɗimbin mutanen da suka dogara da kasuwar wajen harkokin rayuwarsu cikin mawuyacin hali.

Gobarar dai ta tashi ne jiya da yamma daf da lokacin buɗa bakin azumin ramadan, inda ta mamaye rumfuna 135 wadanda aƙasarinsu na kwano da katako ne wasu kuma na itace da kara.

Shugaban hukumar bayar da agajin gaggawa ta jihar Yobe, Dr. Muhammad Goje ya tabbatar da aukuwar wannan gobara.

Ya ƙara da cewa gobarar ba ta shiga shaguna ba kuma ba a rasa rai ko ɗaya ,a a gobarar.

Dr Muhammad Goje ya ƙara da cewa wannan tashin gobara a kasuwar Fika itace ta uku da aka samu a kasuwanni daban-daban cikin kasa da wata daya a jihar ciki harda kasuwar Bukarti, inda rumfuna kusan dari suka ƙone, sai kuma kasuwar Fuchimiran a ƙaramar hukumar Geidam, inda rufunan da gidajen mutane da dama suka kone.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 200 Sun Mutu Sakomakon Girgizar ƙasar a ColombiaShahararren Mawaƙin Najeriya, Davido ya Rubuta wa Trump Wasiƙa Kan Zaɓen Jihar OsunHukumar NHRC ta Buƙaci a Kama Malamin Addinin, Sheikh JingirRundunar sojin Najeriya ta Daƙile Shirin Ƴan Bindiga a FilatoJami'an Ƴan Sanda 10 Sun Mutu Yayin Artabu da Ƴan Bindiga a Jihar KebbiAn Naɗa ɗan Najeriya Gidado Shuaib Wakilin Matasa na IPRA-UN Gabanin GWAEFCC da "Wuce Gona da Iri" da Tambayar 2027: Shin ana Rudar da Tinubu ta Hanyar Mutanen da ke Kewaye da Shi ? Daga Yushau A. ShuaibAn Samu Gawar Yara 3 da guda 1 a Sume a Gidan Mai Maganin GargajiyaMene ne Ainihin Abin da ya faru Aka Rufe Asusun Bankunan Gwamnatin Osun ?Jami'an Tsaro Sun Ceto Mutane 308 a Jihohin Arewacin Najeriya An Kama Mutane 6 da Ake Zargin da Taimaka wa Mayaƙan ISWAP a Jihar BornoZaɓen 2027: PDP ta Miƙa Sunan Jonathan ga INEC a Matsayin ɗan Takararta na Shugaban ƙasaIyanen Babban Jami'in Kula da Harkokin Kuɗaɗen ƙungiyar ISWAP Sun Miƙa Wuya ga SojojiAna Zargin Mayaƙan Boko Haram da Kashe Sojojin Nijar 14Gombe 2027: Malamai da Mambobin APC Sun yi Allah-wadai da Sukar Rarara ga Pantami
X whatsapp