Home Labarai COAS Ya Bukaci Bojojin Nijeriya da su Mayar da Hankali Wajen Kare...

COAS Ya Bukaci Bojojin Nijeriya da su Mayar da Hankali Wajen Kare Rayukan Fararen Hula

Shugaban Rundunar Sojin Kasa ta Najeriya (COAS), Laftanar Janar Waidi Shaibu, ya bukaci jami’ai da dakarun sojin kasar su mutunta hakkin bil’adama tare da ba da fifiko ga kare rayukan fararen hula a dukkan ayyukan soja.

Ya bayyana haka ne yayin da yake batar da Makala mai take (Command Philosophy) ga dakarun da suka halarci kwas a Kwalejin koyon dabarun yaki dake birnin tarayya Abuja a ranar Talata

Shaibu ya jaddada cewa bin dokokin ƙasa da ƙasa da suka shafi yaƙi, ciki har da dokokin jin ƙai na duniya (International Humanitarian Law) da kuma ƙa’idojin aiki na soja wato (Rules of Engagement), ba wai kawai wajibi ne a doka kadai ba, har ma yana da muhimmanci wajen samun nasara a fagen daga.

A cewarsa, wannan tsari zai taimaka wa jami’ai su yi aiki yadda ya kamata a cikin yanayin tsaro mai rikitarwa da ke sauyawa a kullum.

Shaibu, ya bayyana cewa sabbin dabarun aikin sojin Najeriya na ci gaba da inganta bisa yadda rundunar ke tinkarar barazanar tsaro na zamani, musamman irin na yaƙin ‘yan tada ƙayar baya, wanda haɗa kai da fararen hula ke da matuƙar muhimmanci wajen samun nasara.

A nasa jawabin, kwamandan Kwalejin koyon dabarun yaki, Manjo Janar Umar Alkali, ya yabawa COAS bisa ci gaba da bai wa makarantar goyon baya, yana mai cewa jawabin ya ƙara wa mahalarta da makarantar ilimi da kwarewa sosai.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mayaƙan Lakurawa Sun Kashe Sojoji 7 a SokotoAn faɗa wa Shugaba Tinubu Cewa Ina Kitsa Yadda Zan Kashe Shi - ShettimaRundunar 'Yan Sandan Najeriya ta Ceto ƴan Mali 30 Daga Hannun Masu Safarar MutaneMun Kashe Mayaƙan ISIS 175 - Rundunar Sojin NajeriyaFarfesa Pantami ya Janye Daga Takarar Gwamnan Jihar GombeKishiya: Tsakanin ONSA na Ribadu da Tsaron Gida Famadewa Daga Yushau A. ShuaibZaben Fidda Gwani: An Harbe Mutum a Jihar PlateauRundunar 'Yan Sanda ta Tabbatar Kashe Jami'anta 17 a YobeSatar Kayayyakin Banki: An Kama Mutane Huɗu a Jihar Gombe'Yan Bindiga Sun Sace Basarake Tare da Mata 2 a KatsinaJami'an Kwastam Biyu sun Rasa Ransu a Fafatawa da LakurawaMatar Aure ta Zuba wa Kishiyarta da 'Ya'yanta Biyu Fetur Tare da Banka Musu Wuta a KanoIna da ƴancin Mu'amala da Kowa ba Tare da La'akari da Jam'iyya ba - WikeAdadin Masu Fama da Cutar Tamowa na ƙaruwa a Najeriya - MSFGwamnatin Yobe ta Sha Alwashin Kawo ƙarshen Hare-Haren Boko Haram
X whatsapp