Home Labarai COAS Ya Bukaci Bojojin Nijeriya da su Mayar da Hankali Wajen Kare...

COAS Ya Bukaci Bojojin Nijeriya da su Mayar da Hankali Wajen Kare Rayukan Fararen Hula

Shugaban Rundunar Sojin Kasa ta Najeriya (COAS), Laftanar Janar Waidi Shaibu, ya bukaci jami’ai da dakarun sojin kasar su mutunta hakkin bil’adama tare da ba da fifiko ga kare rayukan fararen hula a dukkan ayyukan soja.

Ya bayyana haka ne yayin da yake batar da Makala mai take (Command Philosophy) ga dakarun da suka halarci kwas a Kwalejin koyon dabarun yaki dake birnin tarayya Abuja a ranar Talata

Shaibu ya jaddada cewa bin dokokin ƙasa da ƙasa da suka shafi yaƙi, ciki har da dokokin jin ƙai na duniya (International Humanitarian Law) da kuma ƙa’idojin aiki na soja wato (Rules of Engagement), ba wai kawai wajibi ne a doka kadai ba, har ma yana da muhimmanci wajen samun nasara a fagen daga.

A cewarsa, wannan tsari zai taimaka wa jami’ai su yi aiki yadda ya kamata a cikin yanayin tsaro mai rikitarwa da ke sauyawa a kullum.

Shaibu, ya bayyana cewa sabbin dabarun aikin sojin Najeriya na ci gaba da inganta bisa yadda rundunar ke tinkarar barazanar tsaro na zamani, musamman irin na yaƙin ‘yan tada ƙayar baya, wanda haɗa kai da fararen hula ke da matuƙar muhimmanci wajen samun nasara.

A nasa jawabin, kwamandan Kwalejin koyon dabarun yaki, Manjo Janar Umar Alkali, ya yabawa COAS bisa ci gaba da bai wa makarantar goyon baya, yana mai cewa jawabin ya ƙara wa mahalarta da makarantar ilimi da kwarewa sosai.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 200 Sun Mutu Sakomakon Girgizar ƙasar a ColombiaShahararren Mawaƙin Najeriya, Davido ya Rubuta wa Trump Wasiƙa Kan Zaɓen Jihar OsunHukumar NHRC ta Buƙaci a Kama Malamin Addinin, Sheikh JingirRundunar sojin Najeriya ta Daƙile Shirin Ƴan Bindiga a FilatoJami'an Ƴan Sanda 10 Sun Mutu Yayin Artabu da Ƴan Bindiga a Jihar KebbiAn Naɗa ɗan Najeriya Gidado Shuaib Wakilin Matasa na IPRA-UN Gabanin GWAEFCC da "Wuce Gona da Iri" da Tambayar 2027: Shin ana Rudar da Tinubu ta Hanyar Mutanen da ke Kewaye da Shi ? Daga Yushau A. ShuaibAn Samu Gawar Yara 3 da guda 1 a Sume a Gidan Mai Maganin GargajiyaMene ne Ainihin Abin da ya faru Aka Rufe Asusun Bankunan Gwamnatin Osun ?Jami'an Tsaro Sun Ceto Mutane 308 a Jihohin Arewacin Najeriya An Kama Mutane 6 da Ake Zargin da Taimaka wa Mayaƙan ISWAP a Jihar BornoZaɓen 2027: PDP ta Miƙa Sunan Jonathan ga INEC a Matsayin ɗan Takararta na Shugaban ƙasaIyanen Babban Jami'in Kula da Harkokin Kuɗaɗen ƙungiyar ISWAP Sun Miƙa Wuya ga SojojiAna Zargin Mayaƙan Boko Haram da Kashe Sojojin Nijar 14Gombe 2027: Malamai da Mambobin APC Sun yi Allah-wadai da Sukar Rarara ga Pantami
X whatsapp