Home Labarai Gwamnatin Najeriya ta Caccaki Afrika ta Kudu kan Harin da ake yi...

Gwamnatin Najeriya ta Caccaki Afrika ta Kudu kan Harin da ake yi wa ƴan ƙasarta

Biance Ojukwu

Gwamnatin Najeriya ta Caccaki Afrika ta Kudu kan Harin da ake yi wa ƴan ƙasarta

 

Najeriya ta ce tana nazarin matakan da za ta ɗauka kan Afrika ta Kudu, bayan samun rahotannin kai hare-hare kan ƴan ƙasarta da take shirin fara kwashe su a gobe Laraba.

Ministar harkokin wajen Najeriyar Bianca Ojukwu ta ce gwamnatin ƙasar na duba yiwuwar mayar da martani kan abin da ke faruwa.

Ministar ta ce duk da yake wannan matakin abu ne da za a cimma matsaya kansa nan gaba, amma ana ci gaba da tattaunawa kan abin da ya dace a yi.

Ta zargi hukumomin Afrika ta Kudu da gaza yin komai kan hare-haren da ƴan ƙasarta ke kaiwa Ƴan Najeriya, inda ministar ta ce yawancin waɗanda ke zaune a can suna da takardu kuma sun cika duk wasu ƙa’idojin da suka kamata.

Bianca ta ce sun samu bayanan yadda aka wawushe shagunan ƴan Najeriya da ke sana’o’insu a ƙasar, wasu kuma an cinna wa shagunan nasu wuta tare da haramtawa yaransu zuwa makaranta saboda yadda ake cin zarafinsu.

Ta caccaki gwamnatin Afrika ta Kudu kan yadda har yanzu ba ta fito fili ta yi bayani da kakkausar murya ko ta ɗauki tsattsauran mataki kan abi da ke faruwa ba.

Ministar ta ƙara da cewa Najeriya ba ta ji daɗin hakan ba, ganin yadda ta ba Afrika ta Kudu gudummuwa sosai wajen gwagwarmayar yaki da wariyar launin fata a ƙasar.

Kalama nata na zuwa ne a daidai lokacin da ƴan ci rani ke ci gaba da zaman ɗarɗar a Afrika ta Kudu, inda ƴan ƙasar ke yin zanga-zangar ƙyamar baƙi da kuma buƙatar ƴan kama wuri zauna su bar ƙasar nan da 30 ga watan Yuni.

Shugaban Afrika ta Kudu Cyril Ramaphosa ya sanar da wasu matakai da ƙasar ke ɗauka wajen daƙile kwararar baƙin haure.

Sai dai kuma ya gargaɗi ƴan ƙasarsa da su guji ɗaukar doka a hannunsu.

 

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 200 Sun Mutu Sakomakon Girgizar ƙasar a ColombiaShahararren Mawaƙin Najeriya, Davido ya Rubuta wa Trump Wasiƙa Kan Zaɓen Jihar OsunHukumar NHRC ta Buƙaci a Kama Malamin Addinin, Sheikh JingirRundunar sojin Najeriya ta Daƙile Shirin Ƴan Bindiga a FilatoJami'an Ƴan Sanda 10 Sun Mutu Yayin Artabu da Ƴan Bindiga a Jihar KebbiAn Naɗa ɗan Najeriya Gidado Shuaib Wakilin Matasa na IPRA-UN Gabanin GWAEFCC da "Wuce Gona da Iri" da Tambayar 2027: Shin ana Rudar da Tinubu ta Hanyar Mutanen da ke Kewaye da Shi ? Daga Yushau A. ShuaibAn Samu Gawar Yara 3 da guda 1 a Sume a Gidan Mai Maganin GargajiyaMene ne Ainihin Abin da ya faru Aka Rufe Asusun Bankunan Gwamnatin Osun ?Jami'an Tsaro Sun Ceto Mutane 308 a Jihohin Arewacin Najeriya An Kama Mutane 6 da Ake Zargin da Taimaka wa Mayaƙan ISWAP a Jihar BornoZaɓen 2027: PDP ta Miƙa Sunan Jonathan ga INEC a Matsayin ɗan Takararta na Shugaban ƙasaIyanen Babban Jami'in Kula da Harkokin Kuɗaɗen ƙungiyar ISWAP Sun Miƙa Wuya ga SojojiAna Zargin Mayaƙan Boko Haram da Kashe Sojojin Nijar 14Gombe 2027: Malamai da Mambobin APC Sun yi Allah-wadai da Sukar Rarara ga Pantami
X whatsapp