Home Labarai Gwamnatin Najeriya ta Caccaki Afrika ta Kudu kan Harin da ake yi...

Gwamnatin Najeriya ta Caccaki Afrika ta Kudu kan Harin da ake yi wa ƴan ƙasarta

Biance Ojukwu

Gwamnatin Najeriya ta Caccaki Afrika ta Kudu kan Harin da ake yi wa ƴan ƙasarta

 

Najeriya ta ce tana nazarin matakan da za ta ɗauka kan Afrika ta Kudu, bayan samun rahotannin kai hare-hare kan ƴan ƙasarta da take shirin fara kwashe su a gobe Laraba.

Ministar harkokin wajen Najeriyar Bianca Ojukwu ta ce gwamnatin ƙasar na duba yiwuwar mayar da martani kan abin da ke faruwa.

Ministar ta ce duk da yake wannan matakin abu ne da za a cimma matsaya kansa nan gaba, amma ana ci gaba da tattaunawa kan abin da ya dace a yi.

Ta zargi hukumomin Afrika ta Kudu da gaza yin komai kan hare-haren da ƴan ƙasarta ke kaiwa Ƴan Najeriya, inda ministar ta ce yawancin waɗanda ke zaune a can suna da takardu kuma sun cika duk wasu ƙa’idojin da suka kamata.

Bianca ta ce sun samu bayanan yadda aka wawushe shagunan ƴan Najeriya da ke sana’o’insu a ƙasar, wasu kuma an cinna wa shagunan nasu wuta tare da haramtawa yaransu zuwa makaranta saboda yadda ake cin zarafinsu.

Ta caccaki gwamnatin Afrika ta Kudu kan yadda har yanzu ba ta fito fili ta yi bayani da kakkausar murya ko ta ɗauki tsattsauran mataki kan abi da ke faruwa ba.

Ministar ta ƙara da cewa Najeriya ba ta ji daɗin hakan ba, ganin yadda ta ba Afrika ta Kudu gudummuwa sosai wajen gwagwarmayar yaki da wariyar launin fata a ƙasar.

Kalama nata na zuwa ne a daidai lokacin da ƴan ci rani ke ci gaba da zaman ɗarɗar a Afrika ta Kudu, inda ƴan ƙasar ke yin zanga-zangar ƙyamar baƙi da kuma buƙatar ƴan kama wuri zauna su bar ƙasar nan da 30 ga watan Yuni.

Shugaban Afrika ta Kudu Cyril Ramaphosa ya sanar da wasu matakai da ƙasar ke ɗauka wajen daƙile kwararar baƙin haure.

Sai dai kuma ya gargaɗi ƴan ƙasarsa da su guji ɗaukar doka a hannunsu.

 

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fiye da Kashi 60 na 'Yan Najeriya a Yanzu Suna Rayuwa Cikiin Fatara - IMFGwamnatin Najeriya ta Caccaki Afrika ta Kudu kan Harin da ake yi wa ƴan ƙasartaƳan Bindiga sun Buƙaci Kudin Fansa Kafin Sako Dattijan da Suka je Sulhu a ZamfaraMayaƙan Lakurawa Sun Kashe Sojoji 7 a SokotoAn faɗa wa Shugaba Tinubu Cewa Ina Kitsa Yadda Zan Kashe Shi - ShettimaRundunar 'Yan Sandan Najeriya ta Ceto ƴan Mali 30 Daga Hannun Masu Safarar MutaneMun Kashe Mayaƙan ISIS 175 - Rundunar Sojin NajeriyaFarfesa Pantami ya Janye Daga Takarar Gwamnan Jihar GombeKishiya: Tsakanin ONSA na Ribadu da Tsaron Gida Famadewa Daga Yushau A. ShuaibZaben Fidda Gwani: An Harbe Mutum a Jihar PlateauRundunar 'Yan Sanda ta Tabbatar Kashe Jami'anta 17 a YobeSatar Kayayyakin Banki: An Kama Mutane Huɗu a Jihar Gombe'Yan Bindiga Sun Sace Basarake Tare da Mata 2 a KatsinaJami'an Kwastam Biyu sun Rasa Ransu a Fafatawa da LakurawaMatar Aure ta Zuba wa Kishiyarta da 'Ya'yanta Biyu Fetur Tare da Banka Musu Wuta a Kano
X whatsapp