Home Taska Dakarun Sojin Najeriya Sun Kashe Ƴan Bindiga 3 Sun Ceto Mutane 9...

Dakarun Sojin Najeriya Sun Kashe Ƴan Bindiga 3 Sun Ceto Mutane 9 da akai Garkuwa da su

Rundunar Soji

Dakarun Sojin Najeriya Sun Kashe Ƴan Bindiga 3 Sun Ceto Mutane 9 da akai Garkuwa da su

 

Jami’an tsaron Najeriya sun kashe wasu mutum uku da ake zargin ‘yan bindiga ne, tare da ceto mutum tara da aka yi garkuwa da su a wani samame da suka kai a jihar Kwara, kamar yadda shafin Channels Television mai zaman kansa ya ruwaito a ranar 30 ga Yuli.

An gudanar da samamen ne tare da haɗin gwiwar jami’an Hukumar Tsaro ta Farin Kaya (DSS), dakarun tsaron gandun daji da mafarauta da kuma ‘yan sa-kai a yankunan Obbo-Aiyegunle, Ejiu-Ora da Osi da ke ƙaramar hukumar Ekiti a jihar Kwara, kusa da iyakar jihar Neja.

An yi garkuwa da mutanen ne daga al’ummar Eju, kuma ana cikin tafiya da su ta cikin daji zuwa jihar Neja lokacin da jami’an tsaron suka kai dauki.

Jihar Kwara ta fuskanci ƙaruwa a hare-haren da ake kai wa fararen hula da jami’an tsaro cikin watannin baya-bayan nan.

A ranar 22 ga Yuli, Shugaban Najeriya Bola Tinubu ya amince da kafa sabon bataliyar sojoji a jihar domin yaƙar masu aikata laifuka, ciki har da ‘yan bindiga da kuma ƙungiyar Mahmuda, wadda gwamnati ta bayyana a matsayin wani reshe na Boko Haram..

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Ƴan Bindiga sun kai Hari a Kotun Shari'a da ke Jihar KatsinaBa ma Goyon Bayan a Riƙa Tura Sojoji Domin Aikin Tsaro a Lokacin Zaɓe - INECJam'iyyar NDC ta Buƙaci Sanata Hanga da Gaya da su Sake Tunani Kan Sauya SheƙaYan Bindiga Sun Kashe Kanal Abdussalam Ude Sun Raunata MatarsaMutane 15 Sun Mutu a Sabon Harin Yan Bindiga a Jihar Benue Zaɓen 2027: Uba Sani ya zaɓi MataimakinsaJami'an Tsaro Sun Kuɓutar da Mutane 32 Yayin da 4 Suka Mutu a Jihar Sokoto China ba za ta Bayar ko ta Sayar wa Iran Makamai ba a Kowane h Hali - TrumpBai Dace Obasanjo ya Danganta Marigayi Ghali Na'abba da Zargin Cin Hanci ba - AtikuGarkuwa da Mutane: Dakarun Sojin Najeriya Sun Kama Mutane 5 a Jihar Yobe Sojojin Najeriya na Neman ɗaya Daga Cikin Jami'inta Ruwa a Jallo, Kan Zargin Sayar wa Ƴan bindiga Kakin SojiYaɗa Farfaganda da ƙiyayya Kan Gwamnati ba Zai Kawo ƙarshenta ba - MatawalleMawallafin PRNigeria Ya Fitar Da Littafin Tarihin Rayuwarsa Akan Rigimar NIPSS Yayin Da IMPR Ta Bayyana Cigaba Mai Karfi A Tsakiyar ShekaraShugaban Amurka ya Yaba wa Shugaba Tinubu Kan Matakan da Yake ɗauka Wajen Yaƙi da Ta'addanciBinciken Gaskiya: Shin Gajimaren ne ya ɓulɓulowa ƙasa a Hanyar Abuja Zuwa Kaduna?
X whatsapp