Dakarun Sojin Najeriya Sun Kashe Ƴan Bindiga 3 Sun Ceto Mutane 9 da akai Garkuwa da su
Jami’an tsaron Najeriya sun kashe wasu mutum uku da ake zargin ‘yan bindiga ne, tare da ceto mutum tara da aka yi garkuwa da su a wani samame da suka kai a jihar Kwara, kamar yadda shafin Channels Television mai zaman kansa ya ruwaito a ranar 30 ga Yuli.
Read Also:
An gudanar da samamen ne tare da haɗin gwiwar jami’an Hukumar Tsaro ta Farin Kaya (DSS), dakarun tsaron gandun daji da mafarauta da kuma ‘yan sa-kai a yankunan Obbo-Aiyegunle, Ejiu-Ora da Osi da ke ƙaramar hukumar Ekiti a jihar Kwara, kusa da iyakar jihar Neja.
An yi garkuwa da mutanen ne daga al’ummar Eju, kuma ana cikin tafiya da su ta cikin daji zuwa jihar Neja lokacin da jami’an tsaron suka kai dauki.
Jihar Kwara ta fuskanci ƙaruwa a hare-haren da ake kai wa fararen hula da jami’an tsaro cikin watannin baya-bayan nan.
A ranar 22 ga Yuli, Shugaban Najeriya Bola Tinubu ya amince da kafa sabon bataliyar sojoji a jihar domin yaƙar masu aikata laifuka, ciki har da ‘yan bindiga da kuma ƙungiyar Mahmuda, wadda gwamnati ta bayyana a matsayin wani reshe na Boko Haram..











