Home Taska Ƙungiyar NARD ta yi Barazanar Shiga Yajin Aiki

Ƙungiyar NARD ta yi Barazanar Shiga Yajin Aiki

Ƙungiyar NARD ta yi Barazanar Shiga Yajin Aiki

 

Ƙungiyar Likitoci Masu Neman Ƙwarewa a Najeriya (NARD) ta yi barazanar shiga yajin aiki na sai baba-ta-gani idan har gwamnatin tarayya ba ta biya buƙatunta ba.

NARD ta ce za ta tsunduma yajin aikin ne a ranar 10 ga watan Agusta saboda gaza biyan buƙatunta da suka shafi bashin albashi da inganta walwalarsu da kuma yanayin aiki ba.

Kamar yadda Daily Trust ta ruwaito, ƙungiyar ta cimma wannan matsaya ne a ƙarshen taron Kwamitin zartarwarta da aka gudanar a Gombe daga ranar 26 zuwa 31 ga watan Yuli.

A yayin taron ne wakilan ƙungiyar suka duba yadda aka aiwatar da yarjejeniyoyin da aka cimma da gwamnatin tarayya a baya, tare da nazarin matsalolin da ke addabar fannin lafiya a ƙasar.

Shugaban NARD, Dakta Mohammad Usman Suleiman, ya ce ƙungiyar ta nuna rashin gamsuwa da yadda gwamnatin ke tafiyar hawainiya wajen cika alƙawuran da aka yi, duk da tattaunawa da aka shafe watanni ana yi.

Ya ce ƙungiyar ta tsawaita wa’adin yajin aikin har sau huɗu domin bai wa gwamnati damar warware matsalolin, amma ya ce har yanzu yawancin alƙawuran ba a cika su ba.

 

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Dakarun Sojin Najeriya Sun Kashe Ƴan Bindiga 3 Sun Ceto Mutane 9 da akai Garkuwa da suƳan Bindiga sun kai Hari a Kotun Shari'a da ke Jihar KatsinaBa ma Goyon Bayan a Riƙa Tura Sojoji Domin Aikin Tsaro a Lokacin Zaɓe - INECJam'iyyar NDC ta Buƙaci Sanata Hanga da Gaya da su Sake Tunani Kan Sauya SheƙaYan Bindiga Sun Kashe Kanal Abdussalam Ude Sun Raunata MatarsaMutane 15 Sun Mutu a Sabon Harin Yan Bindiga a Jihar Benue Zaɓen 2027: Uba Sani ya zaɓi MataimakinsaJami'an Tsaro Sun Kuɓutar da Mutane 32 Yayin da 4 Suka Mutu a Jihar Sokoto China ba za ta Bayar ko ta Sayar wa Iran Makamai ba a Kowane h Hali - TrumpBai Dace Obasanjo ya Danganta Marigayi Ghali Na'abba da Zargin Cin Hanci ba - AtikuGarkuwa da Mutane: Dakarun Sojin Najeriya Sun Kama Mutane 5 a Jihar Yobe Sojojin Najeriya na Neman ɗaya Daga Cikin Jami'inta Ruwa a Jallo, Kan Zargin Sayar wa Ƴan bindiga Kakin SojiYaɗa Farfaganda da ƙiyayya Kan Gwamnati ba Zai Kawo ƙarshenta ba - MatawalleMawallafin PRNigeria Ya Fitar Da Littafin Tarihin Rayuwarsa Akan Rigimar NIPSS Yayin Da IMPR Ta Bayyana Cigaba Mai Karfi A Tsakiyar ShekaraShugaban Amurka ya Yaba wa Shugaba Tinubu Kan Matakan da Yake ɗauka Wajen Yaƙi da Ta'addanci
X whatsapp