Ƙungiyar NARD ta yi Barazanar Shiga Yajin Aiki
Ƙungiyar Likitoci Masu Neman Ƙwarewa a Najeriya (NARD) ta yi barazanar shiga yajin aiki na sai baba-ta-gani idan har gwamnatin tarayya ba ta biya buƙatunta ba.
NARD ta ce za ta tsunduma yajin aikin ne a ranar 10 ga watan Agusta saboda gaza biyan buƙatunta da suka shafi bashin albashi da inganta walwalarsu da kuma yanayin aiki ba.
Read Also:
Kamar yadda Daily Trust ta ruwaito, ƙungiyar ta cimma wannan matsaya ne a ƙarshen taron Kwamitin zartarwarta da aka gudanar a Gombe daga ranar 26 zuwa 31 ga watan Yuli.
A yayin taron ne wakilan ƙungiyar suka duba yadda aka aiwatar da yarjejeniyoyin da aka cimma da gwamnatin tarayya a baya, tare da nazarin matsalolin da ke addabar fannin lafiya a ƙasar.
Shugaban NARD, Dakta Mohammad Usman Suleiman, ya ce ƙungiyar ta nuna rashin gamsuwa da yadda gwamnatin ke tafiyar hawainiya wajen cika alƙawuran da aka yi, duk da tattaunawa da aka shafe watanni ana yi.
Ya ce ƙungiyar ta tsawaita wa’adin yajin aikin har sau huɗu domin bai wa gwamnati damar warware matsalolin, amma ya ce har yanzu yawancin alƙawuran ba a cika su ba.










