Home SIYASA Ma’aikatar Bada Agaji ta Kafa Cibiyoyi Takwas Domin Kula da Wadanda su...

Ma’aikatar Bada Agaji ta Kafa Cibiyoyi Takwas Domin Kula da Wadanda su ke Sansanin Gudun Hijira a Garuruwan Zamfara – Kwamishinan Jahar

Ma’aikatar Bada Agaji ta Kafa Cibiyoyi Takwas Domin Kula da Wadanda su ke Sansanin Gudun Hijira a Garuruwan Zamfara – Kwamishinan Jahar

 

Gwamatin Zamfara ta na dawainiya da mutane fiye da 700, 000 da matsalar rashin tsaro ta shafe su.

Ibrahim Magaji Dosara wanda shi ne Kwamishinan yada labaran Zamfara ne ya bayyana wannan.

Kwamishinan tsaro ya ce gwamnatin Muhammad Bello Matawalle ta dauki ‘yan banga har 4200 aiki.

Kaduna – gwamnatin jihar Zamfara ta ce ma’aikatar bada agaji ta kafa cibiyoyi takwas domin kula da wadanda su ke sansanin gudun hijira a garuruwan jihar.

Daily Trust ta rahoto gwamnatin ta na cewa akwai sama da mutane 700, 000 da ke gudun hijira.

Kwamishinan yada labarai na Zamfara, Ibrahim Magaji Dosara ya shaidawa manema labarai a Kaduna cewa gwamnati na dawainiya da masu gudun hijira.

Alhaji Ibrahim Magaji Dosara ya ce a kowace karamar hukuma da ke jihar Zamfara, akwai jami’an bada agaji na gaggawa da aka samar domin su bada taimako.

Wadannan jami’ai za su rika bada tallafi ga wadanda matsalar tsaro ta shafa a kowace karamar hukuma.Akwai kananan hukumomi 14 ne a jihar ta Zamfara.

“Baya ga rabon kayan abinci, katifa, gado, tufafi da sauransu da gwamnatin jiha ta ke yi, ma’aikatar ta na yabon kokarin da kungiyoyin kasashen waje ke yi.”

“Wadannan kungiyoyi su na karfafawa gwamnatin jihar ta hanyar bada kudi ga masu gudun hijira, ana raba N30000 zuwa N40000 ga wadanda abin ya shafa.”

“Gwamnatin tarayya ta narka makudan kudi a kan haka Gwamnatin Zamfara ta na godewa duk wadanda suka taimaka wajen yaye wa mutanenta bakin ciki.” – Alhaji Ibrahim Magaji Dosara

An rahoto kwamishinan yana cewa ana horas da wadanda ‘yan bindiga suka fatattaka.Ana koya masu tukin keke napep, tela, hada ruwa, wanzaci da sauransu.

An dauki ‘yan sa-kai Kwamishinan tsaro da harkokin gida, Mamman Ibrahim Tsafe ya ce sun dauki ma’aikatan sa-kai 4200 aikin banga domin su kare jama’a daga ta’adin ‘yan bindiga.

DIG Mamman Tsafe ya ce an koyawa ma’aikatan rike makami domin su taimakawa jamii’an tsaro.

 

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mayaƙan Lakurawa Sun Kashe Sojoji 7 a SokotoAn faɗa wa Shugaba Tinubu Cewa Ina Kitsa Yadda Zan Kashe Shi - ShettimaRundunar 'Yan Sandan Najeriya ta Ceto ƴan Mali 30 Daga Hannun Masu Safarar MutaneMun Kashe Mayaƙan ISIS 175 - Rundunar Sojin NajeriyaFarfesa Pantami ya Janye Daga Takarar Gwamnan Jihar GombeKishiya: Tsakanin ONSA na Ribadu da Tsaron Gida Famadewa Daga Yushau A. ShuaibZaben Fidda Gwani: An Harbe Mutum a Jihar PlateauRundunar 'Yan Sanda ta Tabbatar Kashe Jami'anta 17 a YobeSatar Kayayyakin Banki: An Kama Mutane Huɗu a Jihar Gombe'Yan Bindiga Sun Sace Basarake Tare da Mata 2 a KatsinaJami'an Kwastam Biyu sun Rasa Ransu a Fafatawa da LakurawaMatar Aure ta Zuba wa Kishiyarta da 'Ya'yanta Biyu Fetur Tare da Banka Musu Wuta a KanoIna da ƴancin Mu'amala da Kowa ba Tare da La'akari da Jam'iyya ba - WikeAdadin Masu Fama da Cutar Tamowa na ƙaruwa a Najeriya - MSFGwamnatin Yobe ta Sha Alwashin Kawo ƙarshen Hare-Haren Boko Haram
X whatsapp