Home SIYASA Ma’aikatar Bada Agaji ta Kafa Cibiyoyi Takwas Domin Kula da Wadanda su...

Ma’aikatar Bada Agaji ta Kafa Cibiyoyi Takwas Domin Kula da Wadanda su ke Sansanin Gudun Hijira a Garuruwan Zamfara – Kwamishinan Jahar

Ma’aikatar Bada Agaji ta Kafa Cibiyoyi Takwas Domin Kula da Wadanda su ke Sansanin Gudun Hijira a Garuruwan Zamfara – Kwamishinan Jahar

 

Gwamatin Zamfara ta na dawainiya da mutane fiye da 700, 000 da matsalar rashin tsaro ta shafe su.

Ibrahim Magaji Dosara wanda shi ne Kwamishinan yada labaran Zamfara ne ya bayyana wannan.

Kwamishinan tsaro ya ce gwamnatin Muhammad Bello Matawalle ta dauki ‘yan banga har 4200 aiki.

Kaduna – gwamnatin jihar Zamfara ta ce ma’aikatar bada agaji ta kafa cibiyoyi takwas domin kula da wadanda su ke sansanin gudun hijira a garuruwan jihar.

Daily Trust ta rahoto gwamnatin ta na cewa akwai sama da mutane 700, 000 da ke gudun hijira.

Kwamishinan yada labarai na Zamfara, Ibrahim Magaji Dosara ya shaidawa manema labarai a Kaduna cewa gwamnati na dawainiya da masu gudun hijira.

Alhaji Ibrahim Magaji Dosara ya ce a kowace karamar hukuma da ke jihar Zamfara, akwai jami’an bada agaji na gaggawa da aka samar domin su bada taimako.

Wadannan jami’ai za su rika bada tallafi ga wadanda matsalar tsaro ta shafa a kowace karamar hukuma.Akwai kananan hukumomi 14 ne a jihar ta Zamfara.

“Baya ga rabon kayan abinci, katifa, gado, tufafi da sauransu da gwamnatin jiha ta ke yi, ma’aikatar ta na yabon kokarin da kungiyoyin kasashen waje ke yi.”

“Wadannan kungiyoyi su na karfafawa gwamnatin jihar ta hanyar bada kudi ga masu gudun hijira, ana raba N30000 zuwa N40000 ga wadanda abin ya shafa.”

“Gwamnatin tarayya ta narka makudan kudi a kan haka Gwamnatin Zamfara ta na godewa duk wadanda suka taimaka wajen yaye wa mutanenta bakin ciki.” – Alhaji Ibrahim Magaji Dosara

An rahoto kwamishinan yana cewa ana horas da wadanda ‘yan bindiga suka fatattaka.Ana koya masu tukin keke napep, tela, hada ruwa, wanzaci da sauransu.

An dauki ‘yan sa-kai Kwamishinan tsaro da harkokin gida, Mamman Ibrahim Tsafe ya ce sun dauki ma’aikatan sa-kai 4200 aikin banga domin su kare jama’a daga ta’adin ‘yan bindiga.

DIG Mamman Tsafe ya ce an koyawa ma’aikatan rike makami domin su taimakawa jamii’an tsaro.

 

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 200 Sun Mutu Sakomakon Girgizar ƙasar a ColombiaShahararren Mawaƙin Najeriya, Davido ya Rubuta wa Trump Wasiƙa Kan Zaɓen Jihar OsunHukumar NHRC ta Buƙaci a Kama Malamin Addinin, Sheikh JingirRundunar sojin Najeriya ta Daƙile Shirin Ƴan Bindiga a FilatoJami'an Ƴan Sanda 10 Sun Mutu Yayin Artabu da Ƴan Bindiga a Jihar KebbiAn Naɗa ɗan Najeriya Gidado Shuaib Wakilin Matasa na IPRA-UN Gabanin GWAEFCC da "Wuce Gona da Iri" da Tambayar 2027: Shin ana Rudar da Tinubu ta Hanyar Mutanen da ke Kewaye da Shi ? Daga Yushau A. ShuaibAn Samu Gawar Yara 3 da guda 1 a Sume a Gidan Mai Maganin GargajiyaMene ne Ainihin Abin da ya faru Aka Rufe Asusun Bankunan Gwamnatin Osun ?Jami'an Tsaro Sun Ceto Mutane 308 a Jihohin Arewacin Najeriya An Kama Mutane 6 da Ake Zargin da Taimaka wa Mayaƙan ISWAP a Jihar BornoZaɓen 2027: PDP ta Miƙa Sunan Jonathan ga INEC a Matsayin ɗan Takararta na Shugaban ƙasaIyanen Babban Jami'in Kula da Harkokin Kuɗaɗen ƙungiyar ISWAP Sun Miƙa Wuya ga SojojiAna Zargin Mayaƙan Boko Haram da Kashe Sojojin Nijar 14Gombe 2027: Malamai da Mambobin APC Sun yi Allah-wadai da Sukar Rarara ga Pantami
X whatsapp