Home SIYASA 2023: Wannan Lokacin ne da Arewa za su Nuna Goyan Baya ga...

2023: Wannan Lokacin ne da Arewa za su Nuna Goyan Baya ga Tinubu – Kashim Shettima

2023: Wannan Lokacin ne da Arewa za su Nuna Goyan Baya ga Tinubu – Kashim Shettima

 

Tsohon gwamnan jihar Borno da ke arewacin Najeriya Sanata Kashim Shettima, ya ce wannan lokacin ne da arewa za su nuna goyon baya ga jagorar jam’iyyar APC mai neman takarar shugabancin Najeriya Asiwaju Bola Ahmed Tinubu.

Sanata Shettima ya bayyana haka ne cikin wata tattaunawa ta musamman da ya yi da jaridar Daily Trust.

Gwamnan wanda na daya daga cikin gwamnonin ANPP uku da suka koma APC bayan rugujewar tasu jam’iyyar lokacin gamayyar da aka yi ta jam’iyyu a zaben 2015, ya jaddada cewa wannan lokaci ne da ya kamata a biya Tinubu wahalar da ya yi na cika dogon burin shugaban Najeriya na yanzu Muhammdu Buhari.

An yi amannar cewa Buhari da Tinubu sune mutum biyu da suka fi kowa mahimmanci a tafiyar APC a 2013, wanda gamayyarsu ta kai ga Buhari ya samu shugabancin Najeriya.

“Babu shakka Buhari na da farin jini a Arewa. Akwai mabiyansa kusan miliyan 15 a yankin. Amma hakan bai sanya ya zama shugaban kasa ba sai da ya hada hannu da yan siyasar sauran bangarorin kudanci da sauran yankuna aka sauya masa fasali tukunna ya zama shugaban kasa a 2015,” in ji Shettima.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp