Home SIYASA 2023: Wannan Lokacin ne da Arewa za su Nuna Goyan Baya ga...

2023: Wannan Lokacin ne da Arewa za su Nuna Goyan Baya ga Tinubu – Kashim Shettima

2023: Wannan Lokacin ne da Arewa za su Nuna Goyan Baya ga Tinubu – Kashim Shettima

 

Tsohon gwamnan jihar Borno da ke arewacin Najeriya Sanata Kashim Shettima, ya ce wannan lokacin ne da arewa za su nuna goyon baya ga jagorar jam’iyyar APC mai neman takarar shugabancin Najeriya Asiwaju Bola Ahmed Tinubu.

Sanata Shettima ya bayyana haka ne cikin wata tattaunawa ta musamman da ya yi da jaridar Daily Trust.

Gwamnan wanda na daya daga cikin gwamnonin ANPP uku da suka koma APC bayan rugujewar tasu jam’iyyar lokacin gamayyar da aka yi ta jam’iyyu a zaben 2015, ya jaddada cewa wannan lokaci ne da ya kamata a biya Tinubu wahalar da ya yi na cika dogon burin shugaban Najeriya na yanzu Muhammdu Buhari.

An yi amannar cewa Buhari da Tinubu sune mutum biyu da suka fi kowa mahimmanci a tafiyar APC a 2013, wanda gamayyarsu ta kai ga Buhari ya samu shugabancin Najeriya.

“Babu shakka Buhari na da farin jini a Arewa. Akwai mabiyansa kusan miliyan 15 a yankin. Amma hakan bai sanya ya zama shugaban kasa ba sai da ya hada hannu da yan siyasar sauran bangarorin kudanci da sauran yankuna aka sauya masa fasali tukunna ya zama shugaban kasa a 2015,” in ji Shettima.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mayaƙan Lakurawa Sun Kashe Sojoji 7 a SokotoAn faɗa wa Shugaba Tinubu Cewa Ina Kitsa Yadda Zan Kashe Shi - ShettimaRundunar 'Yan Sandan Najeriya ta Ceto ƴan Mali 30 Daga Hannun Masu Safarar MutaneMun Kashe Mayaƙan ISIS 175 - Rundunar Sojin NajeriyaFarfesa Pantami ya Janye Daga Takarar Gwamnan Jihar GombeKishiya: Tsakanin ONSA na Ribadu da Tsaron Gida Famadewa Daga Yushau A. ShuaibZaben Fidda Gwani: An Harbe Mutum a Jihar PlateauRundunar 'Yan Sanda ta Tabbatar Kashe Jami'anta 17 a YobeSatar Kayayyakin Banki: An Kama Mutane Huɗu a Jihar Gombe'Yan Bindiga Sun Sace Basarake Tare da Mata 2 a KatsinaJami'an Kwastam Biyu sun Rasa Ransu a Fafatawa da LakurawaMatar Aure ta Zuba wa Kishiyarta da 'Ya'yanta Biyu Fetur Tare da Banka Musu Wuta a KanoIna da ƴancin Mu'amala da Kowa ba Tare da La'akari da Jam'iyya ba - WikeAdadin Masu Fama da Cutar Tamowa na ƙaruwa a Najeriya - MSFGwamnatin Yobe ta Sha Alwashin Kawo ƙarshen Hare-Haren Boko Haram
X whatsapp