Home Taska Gwamnatin Katsina ta Haramta Ayyukan Kungiyar ‘Yan Sa Kai a Fadin Jahar

Gwamnatin Katsina ta Haramta Ayyukan Kungiyar ‘Yan Sa Kai a Fadin Jahar

Gwamnatin Katsina ta Haramta Ayyukan Kungiyar ‘Yan Sa Kai a Fadin Jahar

Gwamnatin jihar katsina da ke arewa maso gabashin Najeriya ta haramta ayyukan kungiyar ‘Yan Sa-kai a fadin jihar baki daya ba tare da wani bata lokaci ba.

A wata sanarwa da mai ba gwamnan jihar shawara na musamman kan harkokin tsaro, Ibrahim Ahmad ya sanya wa hannu, tare da fitarwa a yau Litinin 14 ga watan Fabrairu 2022, gwamnatin ta ce da wannan sanarwa ta umarci ‘yan sanda da sauran jami’an tsaro su rushe wannan kungiya ta ‘Yan Sa Kai a duk fadin jihar.

Gwamnatin ta ce ta yi hakan ne bisa la’akari da azarbabin da ‘yan kungiyar ke yi wajen aikata miyagun laifuka, da hakan ke kai su ga kisan gilla a kan mutanen da ba su ji ba ba su kuma gani ba, tare da kwashe musu kaya da sunan aikin tsaro na ‘Yan Sa Kai.

Sanarwar ta ce daga yanzu gwamnatin jihar ta amince ne kawai da kungiyar ‘yan sintiri ta Vigilante Group, wadda ke karkashin kulawa da saidon ‘yan sanda da sauran hukumomin tsaro da kuma hukumomin gargajiya.

Gwamnatin ta ce daga yanzu ba a yarda kowa ya zartar da wani hukunci da doka ce kawai ya kamata ta yi ba, bisa kowane dalili, illa duk wanda aka kama bisa zargin aikata wani laifi a mika shi ga ‘yan sanda ko wata hukumar tsaro domin daukar matakin da ya dace, idan har akwai bukatar hakan.

 

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp