Home Taska An Samu Matar da ta Warke Daga Cutar Kanjamau a Amurka

An Samu Matar da ta Warke Daga Cutar Kanjamau a Amurka

An Samu Matar da ta Warke Daga Cutar Kanjamau a Amurka

Gamayyar wasu masana kimiyya sun samar da hanyar magance cutar kanjamau a kasar Amurka a yanzu.

Rahoton da kafafen yada labarai na waje suka fitar ya bayyana cewa, an samu matar da ta warke sarai daga kanjamau.

Sai dai, a wasu lokuta a 2009 da 2019 an samu wasu mutanen da suka warke daga cutar, ta wata hanyar daban.

Kasar Amurka – Wata mata da ake kira da ‘Majinyaciyar New York’ domin sakaya sunanta, an ba da rahoton cewa ta zama mace ta farko da ta warke sarai daga cutar kanjamau, TheCable ta tattaro.

An ce an sanar da wannan ci gaban ne a ranar Talata 15 ga watan Fabrairu a wani taro kan cututtuka mai taken: ‘Conference on Retroviruses and Opportunistic Infections’, wanda aka gudanar ta yanar gizo.

A cewar kafar labarai ta NBC, majinyaciyar ta sami magani ne a Cibiyar Kiwon Lafiya ta New York-Presbyterian Weill Cornell a kasar Amurka.

An ce ta kamu da cutar kanjamau a 2013, yayin da aka tabbatar da cewa tana dauke da cutar sankarar bargo a 2017.

Ya lamarin yake?

Hadin maganin, wanda aka ce ya kunshi amfani da jinin da aka dauko daga igiyar cibiya, ya mai da hankali ne ga inganta garkuwar jiki.

Hakazalika, rahoton ya ce, an yi amfani da tsarin jinya na haplo-cord transplant, wanda aka samar don fadada damar samar da maganin ciwon daji ga mutanen da ke da cutar jini.

A cewar jaridar New York Times, duk da cewa masu bincike sun ce suna ci gaba da sanya ido kan yadda ake samun murmurewa daga cutar, amma a cikin watanni 14 da suka gabata ba a gano matar tana dauke da cutar kanjamau ba.

Jinyar ta ya zama mai mahimmanci idan aka yi la’akari da cewa mata sun fi yawa daga cikin mutanen da ke dauke da cutar kanjamau a duniya.

Bisa kididdigar da hadin gwiwar shirin Majalisar Dinkin Duniya kan cutar kanjamau (UNAIDS) ta fitar a 2021, “kashi 53 na dukkan mutanen da ke dauke da cutar kanjamau mata ne da yara mata”.

A baya, kafin wannan sabon ci gaba, an ce wasu maza biyu sun warke sarai daga cutar kanjamau a 2009 da 2019, ta hanyar yi musu dashen bargo.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp