Mogadishu: Mayaƙan Al-Shabab Sun Kai Hare-Hare Babban Birnin Somalia

Mogadishu: Mayaƙan Al-Shabab Sun Kai Hare-Hare Babban Birnin Somalia

Hukumomi a Somalia sun ce da sanyin safiyar yau Laraba mayakan Al-Shabab sun kai hari wani ofishin ‘yan sanda da wurin binciken ababen hawa a Mogadishu babban birnin ƙasar.

Tun tsakar dare ake jin karar harbe-harbe babu kakkautawa a wasu sassan birnin.

Ministan tsaron cikin gida Abdullahi Nor ya wallafa a shafin sada zumunta cewa jami’an tsaro sun yi nasarar murƙushe masu tayar da ƙayar bayan masu alaƙa da kungiyar Al-Qaeda.

Babu rahoton wanda ya jikkata ko asarar rai. A makon da ya wuce mutum shida ne suka mutu lokacin da wani dan kunar-bakin-wake ya ta da bam din da ke jikinsa.

Maharin ya yi nufin tayar da bam ɗin a wata karamar mota da ke dauke da wakilan gwamnati a wurin da ake yin zaben ‘yan majalisu.

Kidnapped School Children

Yauri FGC Students, Kebbi
1190 days 11 hours 54 minutes 31 seconds,

Baptist School Students, Kaduna
1172 days 13 hours 35 minutes 56 seconds

Tegina Islamiya Pupils, Niger (Freed)
Spent 88 days from May 30, 2021 - August 26, 2021


Report By: PRNigeria.com

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here