Hukumar NDLEA ta Kama Makudan Daloli na Jabu a Abuja
Hukumar yaƙi da sha da fataucin miyagun ƙwayoyi ta NDLEA a Najeriya ta ce jami’anta sun kama makudan daloli na jabu a Abuja.
Read Also:
Sanarwar da hukumar ta fitar ta ce an yi yunƙurin sace kusan dala biliyan 2.7 na tattalin arzikin Najeriya ta hanyar tura kuɗaɗen na jabu a kasuwa da suka kai sama da dala miliyan 4.7.
Hukumar ta ce jami’anta sun kama kuɗaɗen a yankin Abaji da aka ɗauko daga Legas zuwa Abuja.
Wannan an kama wanda ake zargi da fataucin kuɗin mai suna Abdulmumini Maikasuwa.
Hukumar ta ce shugabanta Birgediya Janar Buba Marwa ya bayar da umarnin a miƙa kuɗaɗen da wanda ake zargi ga hannun hukumar EFCC domin ci gaba da bincike.
Kidnapped School Children
Yauri FGC Students, Kebbi1462 days 14 hours 26 minutes 22 seconds,
Baptist School Students, Kaduna
1444 days 16 hours 7 minutes 47 seconds
Tegina Islamiya Pupils, Niger (Freed)
Spent 88 days from May 30, 2021 - August 26, 2021
Report By: PRNigeria.com