Home Taska Sarauniyar Ingila ta Kamu da Cutar Corona

Sarauniyar Ingila ta Kamu da Cutar Corona

Sarauniyar Ingila ta Kamu da Cutar Corona

Sarauniya Elizabeth ta Ingila ta kamu da cutar corona, kamar yadda fadar Buckingham ta sanar.

Fadar ta bayyana cewa sarauniya na tattare da alamun sanyi amma ana sa ran za ta ci gaba da gudanar da ayyukanta sama-sama a Windsor a mako mai zuwa.

“Za a ci gaba da duba lafiyarta kuma za a bi duka hanyoyin da suka dace,” kamar yadda fadar ta bayyana a wata sanarwa da ta fitar.

Sarauniya Elizabeth mai shekara 95 ta haɗu da babban ɗanta kuma magajinta wato Yarima Charles wanda shi ma ya kamu da corona a makon da ya gabata.

Sanarwar na zuwa ne mako guda bayan da sarauniyar ta kafa tarihi ta zama wadda ta fi daɗewa kan karagar mulki a tarihin Masarautar Ingila bayan ta cika shekara 70 a kan mulki a ranar 6 ga watan Fabrairu.

Wakilin BBC a Masarautar Ingila Nicholas Witchell ya bayyana cewa babu shakka sarauniya an yi mata riga-kafin corona zagaye na farko da na biyu.

Ya bayyana cewa tana bin rayuwa a hankali a ƴan kwanakin nan tun da ta kwana a asibiti a Oktobar bara yayin da ta je duba lafiyarta.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp