Home Taska Minista Sadiya Umar Farouq ta Jajantawa Waɗanda Gobarar Sansanin ‘Yan Gudun Hijira...

Minista Sadiya Umar Farouq ta Jajantawa Waɗanda Gobarar Sansanin ‘Yan Gudun Hijira ta Shafa a Borno

Minista Sadiya Umar Farouq ta Jajantawa Waɗanda Gobarar Sansanin ‘Yan Gudun Hijira ta Shafa a Borno

 

Ministan Ma’aikatar kula da Al’amuran jin kai da sarrafa annoba da ci gaban al’umma, Ta jajantawa waɗanda gobarar ta shafa.

Maigirma Ministar ma’aikatar Al’amuran jin kai da sarrafa annoba da ci gaban Al’umma, Sadiya Umar Farouq, ta bayyana bakin cikinta kan asarar rayuka da dukiyoyi da aka yi a sansanin ‘yan gudun hijira na Muna El-Badawy, da ke Maiduguri a Jihar Borno.

Hakan na kunshe ne a cikin sanarwar da babban sakataren ma’aikatar, Bashir Nura Alkali ya fitar.

Ministar ta jajantawa iyalan waɗanda suka rasa ‘yan uwansu a gobarar.

A bayanin nata ministar ta kara da cewa, “Rahotannin da suka iso gare ni sun tabbatar da asarar rayuka, an kuma samu lalacewar matsugunai dubu uku (3,000).

Don haka Ministar tace, yawaitar barkewar gobara a Sansanonin ‘Yan gudun hijirar abin damuwa ne kuma Gwamnatin Tarayya da Hukumomin da abin ya shafa a Jihohin za su dauki matakan dakile afkuwar lamarin nan gaba.

A halin da ake ciki, Ministar tace “Na umurci Hukumar Ba da Agajin Gaggawa ta kasa da ta gaggauta aika kayan agaji ga wadanda abin ya shafa a sansanin, yayin da za a gudanar da tantance musabbabin gobarar da ma irin barnar da ta yi.

” Mai girma ministar tayi kira ga mutanen da ke zaune a sansanin ‘yan gudun hijiran da su yi taka-tsan-tsan don hana afkuwar barkewar gobara.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp