Home SIYASA Gwamnan Kwara ya yi Magana Kan Sanya Hijabi Cikin Makarantun Jahar

Gwamnan Kwara ya yi Magana Kan Sanya Hijabi Cikin Makarantun Jahar

Gwamnan Kwara ya yi Magana Kan Sanya Hijabi Cikin Makarantun Jahar

Gwamnan jahar Kwara, Abdulrahman Abdulrazaq, ya bayyana cewa ko shakka babu yana tare da dalibai mata Musulmai kan lamarin sanya Hijabi cikin makarantun jahar.

Yace wannan ita ce matsayarsa saboda shari’o’in da kotu ta yanke kan lamarin da kuma kasancewar Kwara jaha mai daidaito tsakanin addinai kuma jahar da tafi kama da kudu wajen adadin masu addinai mabananta.

Abdulrazaq yace gwamnatinsa kawai doka da gaskiya take bi da kuma nuna adalci tsakanin kowa, sakataren yada labaransa, Rafiu Ajakaye, ya bayyana, rahoton Daily Trust.

Wannan jawabi na Gwamna ya biyo bayan tuhume-tuhumen da Musulmai da Kirista ke yi cewa Gwamnan ya ki bayyana ra’ayinsa kan lamarin saboda siyasa.

Tuni dai iyalan Habeeb Idris, dalibin da aka kashe yayin zanga-zanga a makarantar Oyun Baptsit kwanakin baya sun yi watsi da diyyar N1m da gwamnatin jahar ta basu.

Hakazalika mutum 11 da suka jikkata sun yi watsi da kudi N250,000 da gwamnatin jahar ta basu.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Shin AtikuObi Zasu Iya Tsige TinubuShettima a 2027? Daga Yushau A. ShuaibYadda Shari'ar Masarautar Kano ke Ci gaba da Wakana a Kotun ta ƙoliTawagar Amurka na Shirin Tafiya Pakistan Domin Tattaunawar Sulhu da IranDole Najeriya ta Samu Tsaro ta Kowane Hali - Babban Hafsan TsaroChelsea da Newcastle na Harin Coulibaly, Liverpool na Neman Siyan Marcos SensiBadaƙalar $1.3m: Kotu ta ba EFCC izinin Kama Tsohuwar Ministar jin ƙan Najeriya Sadiya FarouqRaphinha ya Magantu kan Fitar da ƙungiyarsa da aka yi Daga Champion LigRundunar sojin Najeriya ta Musanta bai wa Tsofaffin Mayaƙan Boko Haram MakamaiGwamnatin Tarayya ta Sauya Zarge-Zargen da ta ke yi wa MalamiAn Binne Birgediya Janar Braimah da Sauran Sojojin da Boko Haram ta KasheYaƙin Iran: Hauhawar farashin Kaya a Najeriya ya ƙaruAdadin Matasa 'Yan kwaya da Muka Kama a Shekara 5 - NDLEAJam'iyyar ADC ta Kori Nafi'u Bala GombeRigakafin ƙyanda ya Ceci Yara Miliyan 20 a Afirka - Hukumar Lafiya ta Duniya2027 Ita ce Dama ta ƙarshe da zan Fito Takara - Atiku
X whatsapp