Home SIYASA Kotu ta Kwace Kujerar Gwamnan Jahar Ebonyi da Mataimakinsa Kelechi Igwe

Kotu ta Kwace Kujerar Gwamnan Jahar Ebonyi da Mataimakinsa Kelechi Igwe

Kotu ta Kwace Kujerar Gwamnan Jahar Ebonyi da Mataimakinsa Kelechi Igwe

Gwamna David Umahi na Jihar Ebonyi da mataimakinsa Kelechi Igwe sun rasa kujerunsu saboda ficewa daga jam’iyyar PDP zuwa APC.

Kotun ta yanke hukuncin cewa kuri’un da suka samu yayin zaben gwamna na jam’iyyar PDP ne don haka Umahi da mataimakinsa sun rasa kuri’un bayan ficewarsu daga jam’iyyar.

Kotun ta umurci INEC ta karbi zabin sunayen wadanda za su maye gurbin Umahi da mataimakinsa daga PDP ko kuma ta sake sabon zaben gwamna a jihar.

FCT, Abuja – Babban kotun tarayya da ke zamanta a Abuja, a ranar Talata, a kori Gwamna David Umahi na Jihar Ebonyi da Mataimakinsa Dr Eric Kelechi Igwe, bayan sun fice daga jam’iyyar PDP sun koma APC mai mulkin sa, rahoton Vanguard.

Kotun, a hukuncin da Mai sharia Inyang Ekwo, ya yi, ta ce kuri’u 393,042 da Gwamna Umahi ya samu a zaben ranar 6 ga watan Mari na gwamnan Jihar Ebonyi, na jam’iyyar PDP ne kuma doka bata amince a mayarwa APC ba.

A cewar kotun, bayan komawa jam’iyyar APC, Umahi da mataimakinsa, ba PDP kadai suka bari ba, sun raba kansu da kuri’u jam’iyyar ta PDP, Daily Trust ta rahoto.

Kotun ta ce idan aka yi la’akari da sakamakon zaben na gwamna, kujerar gwamnan Jihar Ebonyi da mataimakinsa, ‘mallakar wanda suka yi karar ne ba wata jam’iyyar daban ba.’

“Babu wani tanadi a kundin tsarin mulkin kasa da ya nuna ana iya musayar kuri’u daga jam’iyya daya zuwa wata jam’iyyar.”

Ta ce jam’iyyar PDP ce ke da kuri’un da kujerun da masu zabe a Jihar Ebonyi suka kada, don haka ba za a iya mika wa Gwamna Umahi da mataimkinsa kuri’un ba idan sun fice daga jam’iyyar.

Don haka kotun ta bada umurnin cewa nan take Dave Umahi da Igwe su ajiye mukamansu.

Kotu ta umurci INEC ta karbi sunayen wadanda za su maye Umahi da mataimakinsa daga PDP ko ta sake sabon zabe

Ta kuma umurci hukumar zabe mai zaman kanta INEC ta karbi sunayen mutanen za su maye gurbin Umahi da mataimakinsa daga PDP, ko kuma ta sake yin sabon zabe a jihar Ebonyi kamar yadda sashi na 177(c) na kundin tsarin mulki da aka yi wa kwaskwarima ya ce.

Kotun ta kuma hana Umahi da mataimakinsa Igwe cigaba da amsa sunan gwamna da mataimakinsa na jihar Ebonyi.

Kotun ta yanke hukuncin ne bayan karar da jam’iyyar PDP ta shigar bayan Umahi da mataimakinsa sun koma APC.

Saurari karin bayani …

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 6 Sun Rasu 4 Sun Jilkata Sanadiyyar Tsawa a Jihar AdamawaMatatar Dangote ta Dakatar da Amfani da Naira Wajen Sayar da Man FeturZaɓen 2027: Jam'iyyar ADC ta Mayar da Martani kan Hukuncin Kotu Akwai Yiwuwar ba zan kai Lokacin Zaɓen 2027 ba - ObiHukuncin da Kotu ta Yanke wa Direban Keke Napep Kan Aikata Fyaɗeɓata Sunan Gwamnatin Katsina: Kotu ta buƙaci Ƴan Sanda su Tsare Dr Kurfi Gwamnonin Arewacin Najeriya sun Kafa Gidauniyar Yaƙi da Matsalar TsaroGwamnatin Tarayya ba ta Yanke Hukuncin Sauya Kayan NYSC ba - Ministan MatasaJuyin Mulki: DSS ta Gurfanar da Mutane 5 kan ɓoye Timipre Sylva Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 2 Tare da Limami a Jihar Sokoto Dakarun Soji Sun Bankaɗo Wajen ƙera da Rarraba Bindigogi ga Ƴan Ta'addaJami'an DSS Sun Kama Tsohon Ministan Kimiyya da Fasaha, Uche NnajiYan Bindiga Sun Hallaka Mutane 10 a Jihar BenueNMDPRA ta Gargaɗi Gidajen Man da ba su Rage Farashi ba NECO: ɗalibai 35 na Hannun Ƴan Bindiga - Ƴan Sanda 
X whatsapp