Home SIYASA APC ta Mutu, Allah ya ji Kanta – Dino Melaye

APC ta Mutu, Allah ya ji Kanta – Dino Melaye

Lagos
Akinwunmi-Ambode lagos Governor

APC ta Mutu, Allah ya ji Kanta – Dino Melaye

 

A yanzu haka, rikicin shugabanci ya baibaye jam’iyyar APC gabannin babban taronta na kasa.

Sanata Dino Melaye ya yi amfani da wannan damar wajen yi mata ba’a, inda ya ce an yi juyin mulki a jam’iyyar mai mulki.

Ya kuma sanar a shafinsa na soshiyal midiya cewa APC ta mutu tare da yi mata addu’an samun rahama

Gabannin babban taron jam’iyyar All Progressives Congress (APC) wanda za a yi a ranar 26 ga watan Maris, sabon rikicin shugabanci ya kunno kai a jam’iyyar mai mulki.

Hakan ya biyo bayan darewa kujerar Gwamna Mai Mala Buni da Gwamna Sani Bello na jihar Neja ya yi a matsayin shugaban riko na jam’iyyar ta kasa, a ranar Litinin, 7 ga watan Maris.

Wannan ya sa Sanata Dino Melaye, tsohon dan majalisa da ya wakilci Kogi ta yamma a majalisar dattawa, yiwa jam’iyyar mai mulki ba’a.

An yi juyin mulki a APC – Dino Melaye

Dino ya je shafinsa na Instagram inda ya yi wani rubutu kan rikicin na APC sannan ya ce an yi juyin mulki a jam’iyyar mai mulki.

Ya ce: “Kwace ya kwace daga hannun wanda ya kwace….yepaaaaa. Juyin mulki a APC.”

APC ta mutu, Allah ya ji kanta

Dan siyasar bai tsaya a nan ba, ya kuma wallafa cewa APC ta mutu tare da yi mata addu’an Allah ya ji kanta.

Ya rubuta a shafin nasa:

“RIP APC: 2014 – 2022. Shekaru 8. Kin tafi da wuri haka. Mai sanarwa – SDM”

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mayaƙan Lakurawa Sun Kashe Sojoji 7 a SokotoAn faɗa wa Shugaba Tinubu Cewa Ina Kitsa Yadda Zan Kashe Shi - ShettimaRundunar 'Yan Sandan Najeriya ta Ceto ƴan Mali 30 Daga Hannun Masu Safarar MutaneMun Kashe Mayaƙan ISIS 175 - Rundunar Sojin NajeriyaFarfesa Pantami ya Janye Daga Takarar Gwamnan Jihar GombeKishiya: Tsakanin ONSA na Ribadu da Tsaron Gida Famadewa Daga Yushau A. ShuaibZaben Fidda Gwani: An Harbe Mutum a Jihar PlateauRundunar 'Yan Sanda ta Tabbatar Kashe Jami'anta 17 a YobeSatar Kayayyakin Banki: An Kama Mutane Huɗu a Jihar Gombe'Yan Bindiga Sun Sace Basarake Tare da Mata 2 a KatsinaJami'an Kwastam Biyu sun Rasa Ransu a Fafatawa da LakurawaMatar Aure ta Zuba wa Kishiyarta da 'Ya'yanta Biyu Fetur Tare da Banka Musu Wuta a KanoIna da ƴancin Mu'amala da Kowa ba Tare da La'akari da Jam'iyya ba - WikeAdadin Masu Fama da Cutar Tamowa na ƙaruwa a Najeriya - MSFGwamnatin Yobe ta Sha Alwashin Kawo ƙarshen Hare-Haren Boko Haram
X whatsapp