Home SIYASA Gwamnan Jahar Ebonyi David Umahi ya ɗaukaka Kara Kan Tsige Shi Daga...

Gwamnan Jahar Ebonyi David Umahi ya ɗaukaka Kara Kan Tsige Shi Daga Mulki

Gwamnan Jahar Ebonyi David Umahi ya ɗaukaka Kara Kan Tsige Shi Daga Mulki

Gwamnan jahar Ebonyi David Umahi da ke kudu maso gabashin Najeriya ya daukaka kara game da hukuncin wata babbar kotun tarayya wadda ta bayar da umurnin sauke shi daga mulki bisa sauya sheka da ya yi daga jam’iyyar PDP zuwa APC.

Takardar da suka gabatar ta daukaka karar, ta ce kotun ta yi kuskure a hukuncin da ta yanke, saboda haka ne ya ce yana da ja da daukacin shari’ar.

Takardar ta ce kotun ta gaza bisa dogaron da ta yi da sashen na 68, da na 109 na kundin tsarin Mulki wanda dole gwamnan ya bar mukaminsa kasancewar ya sauya sheka daga jam’iyyar PDP wadda aka zabe shi a karkashinta, zuwa jam’iyyar APC mai mulkin kasar, wanda hakan a cewar takardar tamkar watsi ne da wani hukunci da kotun kolin kasar ta taba yankewa, tsakanin ministan shari’a na Najeriya da tsohon mataimakain shugaban kasa Atiku Abubakar, inda ta ce babu wani tanadin kundin tsarin mulki da ya haramta wa shugaban kasa, ko mataimakinsa, ko kuma gwamnan, ko mataimakinsa daga sauya sheka daga wata jam’iyya zuwa wata.

 

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Shin AtikuObi Zasu Iya Tsige TinubuShettima a 2027? Daga Yushau A. ShuaibYadda Shari'ar Masarautar Kano ke Ci gaba da Wakana a Kotun ta ƙoliTawagar Amurka na Shirin Tafiya Pakistan Domin Tattaunawar Sulhu da IranDole Najeriya ta Samu Tsaro ta Kowane Hali - Babban Hafsan TsaroChelsea da Newcastle na Harin Coulibaly, Liverpool na Neman Siyan Marcos SensiBadaƙalar $1.3m: Kotu ta ba EFCC izinin Kama Tsohuwar Ministar jin ƙan Najeriya Sadiya FarouqRaphinha ya Magantu kan Fitar da ƙungiyarsa da aka yi Daga Champion LigRundunar sojin Najeriya ta Musanta bai wa Tsofaffin Mayaƙan Boko Haram MakamaiGwamnatin Tarayya ta Sauya Zarge-Zargen da ta ke yi wa MalamiAn Binne Birgediya Janar Braimah da Sauran Sojojin da Boko Haram ta KasheYaƙin Iran: Hauhawar farashin Kaya a Najeriya ya ƙaruAdadin Matasa 'Yan kwaya da Muka Kama a Shekara 5 - NDLEAJam'iyyar ADC ta Kori Nafi'u Bala GombeRigakafin ƙyanda ya Ceci Yara Miliyan 20 a Afirka - Hukumar Lafiya ta Duniya2027 Ita ce Dama ta ƙarshe da zan Fito Takara - Atiku
X whatsapp