Home SIYASA Na Janye  Daga Neman Takarar  Shugbancin Jam’iyyar APC – Ali Modu Sheriff

Na Janye  Daga Neman Takarar  Shugbancin Jam’iyyar APC – Ali Modu Sheriff

Na Janye  Daga Neman Takarar  Shugbancin Jam’iyyar APC – Ali Modu Sheriff

 

Tsohon gwamnan Borno da ke arewa maso gabas, Ali Modu Sheriff, ya ce ya janye daga takarar neman shugbancin jam’iyyar APC mai mulki a Najeriya.

Modu Sheriff ya faɗa wa BBC Hausa cewa ya janye takarar ce saboda biyayya ga Shugaban Ƙasa Muhammadu Buhari.

“Shugaban ƙasa na son shugaban jam’iyya ya fito daga Arewa ta Tsakiya. Shugabanmu ne, babanmu ne, duk abin da yake so shi za mu yi. Ni ba na jayayya da iyayena a kowane fanni,” in ji shi.

Matakin tsohon gwamnan na zuwa ne bayan jam’iyyar ta ce ta ware wa shiyyar arewa ta tsakiya muƙamin shugaba na ƙasa yayin ganawar da gwamnoninta suka yi da Shugaba Buhari a watan Fabarairu.

An ware wa shiyyoyin Arewa muƙaman da na Kudu suka riƙe a cikin shekara takwas da suka wuce, su ma na Kudu haka, a cewar Gwamnan Kaduna Nasir El-Rufai.

Bisa wannan tsari ne jam’iyyar za ta zaɓi ssabbin shugabanninta a babban taron da za ta gudanar ranar 26 ga watan Maris.

‘Matakin da zan ɗauka nan gaba’

Ali Modu Sharif ya gode wa dukkan mutanen da suka goya masa baya”, amma ya ce ba zai daina siyasa ba.

“Ina jira daga nan zuwa Juma’a, idan jam’iyya ta ce kowane yanki zai iya tsayawa takara ina nan,” a cewarsa.

Da aka tambaye shi ko zai bar siyasa, sai ya amsa da cewa: “Ba zan bar siyasa ba. Don me zan bar siyasa?

“Ba zan nemi wani muƙami ba sai na shugaban jam’iyya saboda na taimaka wa jam’iyyarmu mai girma.”

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp