Home SIYASA Na Janye  Daga Neman Takarar  Shugbancin Jam’iyyar APC – Ali Modu Sheriff

Na Janye  Daga Neman Takarar  Shugbancin Jam’iyyar APC – Ali Modu Sheriff

Na Janye  Daga Neman Takarar  Shugbancin Jam’iyyar APC – Ali Modu Sheriff

 

Tsohon gwamnan Borno da ke arewa maso gabas, Ali Modu Sheriff, ya ce ya janye daga takarar neman shugbancin jam’iyyar APC mai mulki a Najeriya.

Modu Sheriff ya faɗa wa BBC Hausa cewa ya janye takarar ce saboda biyayya ga Shugaban Ƙasa Muhammadu Buhari.

“Shugaban ƙasa na son shugaban jam’iyya ya fito daga Arewa ta Tsakiya. Shugabanmu ne, babanmu ne, duk abin da yake so shi za mu yi. Ni ba na jayayya da iyayena a kowane fanni,” in ji shi.

Matakin tsohon gwamnan na zuwa ne bayan jam’iyyar ta ce ta ware wa shiyyar arewa ta tsakiya muƙamin shugaba na ƙasa yayin ganawar da gwamnoninta suka yi da Shugaba Buhari a watan Fabarairu.

An ware wa shiyyoyin Arewa muƙaman da na Kudu suka riƙe a cikin shekara takwas da suka wuce, su ma na Kudu haka, a cewar Gwamnan Kaduna Nasir El-Rufai.

Bisa wannan tsari ne jam’iyyar za ta zaɓi ssabbin shugabanninta a babban taron da za ta gudanar ranar 26 ga watan Maris.

‘Matakin da zan ɗauka nan gaba’

Ali Modu Sharif ya gode wa dukkan mutanen da suka goya masa baya”, amma ya ce ba zai daina siyasa ba.

“Ina jira daga nan zuwa Juma’a, idan jam’iyya ta ce kowane yanki zai iya tsayawa takara ina nan,” a cewarsa.

Da aka tambaye shi ko zai bar siyasa, sai ya amsa da cewa: “Ba zan bar siyasa ba. Don me zan bar siyasa?

“Ba zan nemi wani muƙami ba sai na shugaban jam’iyya saboda na taimaka wa jam’iyyarmu mai girma.”

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 6 Sun Rasu 4 Sun Jilkata Sanadiyyar Tsawa a Jihar AdamawaMatatar Dangote ta Dakatar da Amfani da Naira Wajen Sayar da Man FeturZaɓen 2027: Jam'iyyar ADC ta Mayar da Martani kan Hukuncin Kotu Akwai Yiwuwar ba zan kai Lokacin Zaɓen 2027 ba - ObiHukuncin da Kotu ta Yanke wa Direban Keke Napep Kan Aikata Fyaɗeɓata Sunan Gwamnatin Katsina: Kotu ta buƙaci Ƴan Sanda su Tsare Dr Kurfi Gwamnonin Arewacin Najeriya sun Kafa Gidauniyar Yaƙi da Matsalar TsaroGwamnatin Tarayya ba ta Yanke Hukuncin Sauya Kayan NYSC ba - Ministan MatasaJuyin Mulki: DSS ta Gurfanar da Mutane 5 kan ɓoye Timipre Sylva Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 2 Tare da Limami a Jihar Sokoto Dakarun Soji Sun Bankaɗo Wajen ƙera da Rarraba Bindigogi ga Ƴan Ta'addaJami'an DSS Sun Kama Tsohon Ministan Kimiyya da Fasaha, Uche NnajiYan Bindiga Sun Hallaka Mutane 10 a Jihar BenueNMDPRA ta Gargaɗi Gidajen Man da ba su Rage Farashi ba NECO: ɗalibai 35 na Hannun Ƴan Bindiga - Ƴan Sanda 
X whatsapp