Home WASANNI Newcastle United na Son Daukar Neymar Daga PSG

Newcastle United na Son Daukar Neymar Daga PSG

Newcastle United na Son Daukar Neymar Daga PSG

 

An ruwaito cewar Newcastle United na duba hanyar da za ta dauko Neymar daga Paris St Germain a karshen kakar bana.

Newcastle wadda aka sayar da ita, ta saka kudi mai tsoka wajen sayo ‘yan wasan da za su kara karfin kungiyar, ciki har da dan kwallon Brazil, Neymar da take son dauka a karshen kakar nan.

Kamar yadda The Sun ta wallafa, Newcastle na bibiyar halin da Neymar ke ciki a PSG, tana kuma son yi masa tayin kudi mai tsoka, domin ya koma buga gasar Premier League.

Bayan da aka yi waje da PSG daga Champions League a bana a hannun Real Madrid, magoya bayan kungiyar Faransa kan yi wa wasu ‘yan wasan ihu a lokacin da suke buga mata leda, ciki har da Neymar.

Tun farko Neymar bai samu alaka mai kyau da PSG da kuma magoya bayanta ba, duk da kwazon da yake yi wa kungiyar, hakan ne Newcastle taga ya dace ta yi wa dan wasan Brazil tayin kudi mai tsoka, watakila ya samu buga babbar gasar tamaula ta Ingila cikin natsuwa.

Neymar yana da kunshin yarjejeniya da PSG wadda za ta kare a karshen kakar 2025, ana kuma ganin Newcastle za ta iya biyan albashin dan wasan na Yuro 500,000 duk mako idan ya amince ya koma kungiyar da taka leda.

 

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp