Home SIYASA Da Fadin Cigaba a Baki Zai Kawo Cigaba, da Mun Kasance Kasa...

Da Fadin Cigaba a Baki Zai Kawo Cigaba, da Mun Kasance Kasa Mafi Cigaba a Duniya – Tinubu

Da Fadin Cigaba a Baki Zai Kawo Cigaba, da Mun Kasance Kasa Mafi Cigaba a Duniya – Tinubu

 

Jigon jam’iyyar APC, Bola Tinubu, ya bayyana cewa lokaci ya yi da ya kamata yan Najeriya su fadawa juna gaskiya.

Asiwaju Bola Tinubu, ya bayyana niyyar takarar kujeran shugaban kasa a zaben Febrairun 2023.

Tinubu ya bada kyautar cibiyar karatu na kimanin kudi biliyan daya ga jami’ar jihar Legas LASU.

Legas – Mai niyyar takarar kujerar shugaban kasa a 2023 kuma tsohon gwamnan jihar Legas, Asiwaju Bola Tinubu, ya bayyana cewa dukkanmu muka kashe Najeriya kuma mu zamu iya gyarata.

Ya bayyana hakan ne ranar Alhamis a lakcan bikin yaye daliban jami’ar jihar Legas LASU.

Ya samu wakilcin mataimakin gwamnan jihar Legas, Dr Obafemi Hamzat, rahoton Vanguard.

Yace:

“Mu daina yaudarar kawunanmu. Mun dade muna ikirarin cewa muna da arziki kuma gobe zamu ji dadi amma shekaru na taf iya kuma babu cigaba.”

“Da fadin cigaba a baki zai kawo cigaba, da mun kasance kasa mafi cigaba a duniya.”

“Amma kash, Najeriya na waje guda. Mun zama masu fitar da dukiyarmu amma mu shigo da kaya da tsada.”

“Wajibi ne mu fadawa juna gaskiya, mu fuskancesa mu gyara. Dukkan mu muka janyo kuma zamu iya zama mafita. Mu hada kai. Wajibi ne mu gyara kasar nan.”

A kan rashin aikin yin matasa, Tinubu ya ce rashin aiki da aiki babu albashin kwarai tsakanin matasa ya kai 60%, kuma wajibi ne a magance hakan.

Tinubu yace samawa matashin birane aikin yi, aikin noma, harkar gidaje, ilimi, tattalin arziki da manyan ayyuka ya kamata gwamnati ta mayar da hankali.

Tinubu ya bada kyautar cibiyar karatu na kimanin kudi biliyan daya ga makarantar.

 

 

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp