Home SIYASA Da Fadin Cigaba a Baki Zai Kawo Cigaba, da Mun Kasance Kasa...

Da Fadin Cigaba a Baki Zai Kawo Cigaba, da Mun Kasance Kasa Mafi Cigaba a Duniya – Tinubu

Da Fadin Cigaba a Baki Zai Kawo Cigaba, da Mun Kasance Kasa Mafi Cigaba a Duniya – Tinubu

 

Jigon jam’iyyar APC, Bola Tinubu, ya bayyana cewa lokaci ya yi da ya kamata yan Najeriya su fadawa juna gaskiya.

Asiwaju Bola Tinubu, ya bayyana niyyar takarar kujeran shugaban kasa a zaben Febrairun 2023.

Tinubu ya bada kyautar cibiyar karatu na kimanin kudi biliyan daya ga jami’ar jihar Legas LASU.

Legas – Mai niyyar takarar kujerar shugaban kasa a 2023 kuma tsohon gwamnan jihar Legas, Asiwaju Bola Tinubu, ya bayyana cewa dukkanmu muka kashe Najeriya kuma mu zamu iya gyarata.

Ya bayyana hakan ne ranar Alhamis a lakcan bikin yaye daliban jami’ar jihar Legas LASU.

Ya samu wakilcin mataimakin gwamnan jihar Legas, Dr Obafemi Hamzat, rahoton Vanguard.

Yace:

“Mu daina yaudarar kawunanmu. Mun dade muna ikirarin cewa muna da arziki kuma gobe zamu ji dadi amma shekaru na taf iya kuma babu cigaba.”

“Da fadin cigaba a baki zai kawo cigaba, da mun kasance kasa mafi cigaba a duniya.”

“Amma kash, Najeriya na waje guda. Mun zama masu fitar da dukiyarmu amma mu shigo da kaya da tsada.”

“Wajibi ne mu fadawa juna gaskiya, mu fuskancesa mu gyara. Dukkan mu muka janyo kuma zamu iya zama mafita. Mu hada kai. Wajibi ne mu gyara kasar nan.”

A kan rashin aikin yin matasa, Tinubu ya ce rashin aiki da aiki babu albashin kwarai tsakanin matasa ya kai 60%, kuma wajibi ne a magance hakan.

Tinubu yace samawa matashin birane aikin yi, aikin noma, harkar gidaje, ilimi, tattalin arziki da manyan ayyuka ya kamata gwamnati ta mayar da hankali.

Tinubu ya bada kyautar cibiyar karatu na kimanin kudi biliyan daya ga makarantar.

 

 

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Shin AtikuObi Zasu Iya Tsige TinubuShettima a 2027? Daga Yushau A. ShuaibYadda Shari'ar Masarautar Kano ke Ci gaba da Wakana a Kotun ta ƙoliTawagar Amurka na Shirin Tafiya Pakistan Domin Tattaunawar Sulhu da IranDole Najeriya ta Samu Tsaro ta Kowane Hali - Babban Hafsan TsaroChelsea da Newcastle na Harin Coulibaly, Liverpool na Neman Siyan Marcos SensiBadaƙalar $1.3m: Kotu ta ba EFCC izinin Kama Tsohuwar Ministar jin ƙan Najeriya Sadiya FarouqRaphinha ya Magantu kan Fitar da ƙungiyarsa da aka yi Daga Champion LigRundunar sojin Najeriya ta Musanta bai wa Tsofaffin Mayaƙan Boko Haram MakamaiGwamnatin Tarayya ta Sauya Zarge-Zargen da ta ke yi wa MalamiAn Binne Birgediya Janar Braimah da Sauran Sojojin da Boko Haram ta KasheYaƙin Iran: Hauhawar farashin Kaya a Najeriya ya ƙaruAdadin Matasa 'Yan kwaya da Muka Kama a Shekara 5 - NDLEAJam'iyyar ADC ta Kori Nafi'u Bala GombeRigakafin ƙyanda ya Ceci Yara Miliyan 20 a Afirka - Hukumar Lafiya ta Duniya2027 Ita ce Dama ta ƙarshe da zan Fito Takara - Atiku
X whatsapp