Home SIYASA Gwamna Obaseki ya Kori Ma’aikata 513 Daga Bakin Aiki

Gwamna Obaseki ya Kori Ma’aikata 513 Daga Bakin Aiki

Gwamna Obaseki ya Kori Ma’aikata 513 Daga Bakin Aiki

 

Gwamnan jihar Edo, Godwin Obaseki, ya amince da korar ma’aikata 513 daga bakin aiki waɗan da ke sashin harkokin wasanni.

A wani kundi mai ɗauke da sanarwan korar ma’aikatan, gwamnan ya ce ya ɗauki wannan matakin domin garambawul ga sashin.

Ma’aikatan da korar ta shafa da suka haɗa da yan wasa da masu horarwa da shugabanni, sun fantsama tituna suna zanga-zanga ranar Laraba.

Edo- Gwamna Godwin Obaseki na jihar Edo, ya sallami ma’aikata 513 na sashin wasanni na jihar kuma matakin ya fara aiki tun daga Litinin 21 ga watan Maris, 2022.

Sallamar aikin a cewar rahoton Vanguard, na cikin wata sanarwa da gwamnatin ta fitar ranar 4 ga watan Maris, 2022, kuma waɗan da lamarin ya shafa ya kunshi manya da ƙananan ma’aikata.

Legit.ng Hausa ta gano gwamnatin na cewa matakin wani bangare ne na kokarin da take na canza salon sashin wasanni zuwa hukumar wasanni ta jihar Edo.

Zamu biya ma’aikatan da aka kora haƙƙinsu – Gwmanati

Sanarwan ta ƙara da cewa gwamnati zata biya ma’ikatan da korar ta shafa hakkokinsu na albashin wata ɗaya.

Hakanan ta ce za’a fara biyan ma’aikatan kuɗin Fanshon su a watan Afrilu, 2020, a rahoton Leadership ma’ikatan da aka sallama sun kai 514.

Ma’aikatan da matakin sallamar ya shafa sun haɗa da, yan wasan guje-guje da tsalle-tsalle, masu horarwa da kuma na ɓangaren shugabanci.

Wane mataki ma’aikatan suka ɗauka?

A ranar 24 ga watan Maris, 2022, ma’aikatan da gwamnan ya kora suka fito gagarumar zanga-zanga a kewayen filin Samuel Ogbemudia da wasu tituna dake kusa.

Wasu daga cikin mutanen sun ce sun yi mamakin ganin sanarwan cewa an sallame su daga aiki, kuma aka ba su shawaran su sake neman aiki na wucin gadi.

Ɗaya daga cikin yan zanga-zangan, Patience Igbiti, ta ce:

“Sama da shekara 20 ina aiki a matsayin cikakkiyar ma’aikaciya kuma lokaci guda suka kore ni. Na ƙi karban ayyuka da dama a ƙasar waje domin na yi wa jihata aiki. Daga ina ake son na fara yanzu?”

Haka nan kuma wani ma’aikacin da lamarin ya shafa, Friday Aibangbe, ya ce:

“Ina da kwarin guiwar cewa gwamna bai damu da mu ba kwata-kwata. Mun masa aiki muka zaɓe shi kuma muka sadaukar domin shi, amma abin da ya saka mana da shi kenan yanzu.”

Da yake jawabi ga masu zanga-zanga, shugaban hukumar wasanni, Yusuf Ali, ya ɗau alƙawarin kai korafinsu ga gwamnatin jiha.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Shin AtikuObi Zasu Iya Tsige TinubuShettima a 2027? Daga Yushau A. ShuaibYadda Shari'ar Masarautar Kano ke Ci gaba da Wakana a Kotun ta ƙoliTawagar Amurka na Shirin Tafiya Pakistan Domin Tattaunawar Sulhu da IranDole Najeriya ta Samu Tsaro ta Kowane Hali - Babban Hafsan TsaroChelsea da Newcastle na Harin Coulibaly, Liverpool na Neman Siyan Marcos SensiBadaƙalar $1.3m: Kotu ta ba EFCC izinin Kama Tsohuwar Ministar jin ƙan Najeriya Sadiya FarouqRaphinha ya Magantu kan Fitar da ƙungiyarsa da aka yi Daga Champion LigRundunar sojin Najeriya ta Musanta bai wa Tsofaffin Mayaƙan Boko Haram MakamaiGwamnatin Tarayya ta Sauya Zarge-Zargen da ta ke yi wa MalamiAn Binne Birgediya Janar Braimah da Sauran Sojojin da Boko Haram ta KasheYaƙin Iran: Hauhawar farashin Kaya a Najeriya ya ƙaruAdadin Matasa 'Yan kwaya da Muka Kama a Shekara 5 - NDLEAJam'iyyar ADC ta Kori Nafi'u Bala GombeRigakafin ƙyanda ya Ceci Yara Miliyan 20 a Afirka - Hukumar Lafiya ta Duniya2027 Ita ce Dama ta ƙarshe da zan Fito Takara - Atiku
X whatsapp