Home Taska Yanayin Tsaro: Baya ga Azman, Kamfanin Jiragen Sama na Air Peace ya...

Yanayin Tsaro: Baya ga Azman, Kamfanin Jiragen Sama na Air Peace ya Dakatar da Aiki a Kaduna

Yanayin Tsaro: Baya ga Azman, Kamfanin Jiragen Sama na Air Peace ya Dakatar da Aiki a Kaduna

 

Jaridar Daily Trust ta rahoto cewa, kamfanin jiragen sama na Air Peace ya dakatar da ayyukansa zuwa filin jirgin sama na Kaduna.

Wata majiya ta alakanta faruwar lamarin ga harin da aka kai a kusa da filin jirgin Kaduna a karshen makon jiya.

Idan baku manta ba, an ruwaito yadda wasu ‘yan bindiga suka bindige wani mai gadi da ke aiki a hukumar kula da sararin samaniyar Najeriya a ranar Asabar.

Sojoji sun yi artabu da ‘yan ta’addan, lamarin da ya janyo tsaikon tashin jirgin sama na Azman da ke kan hanyarsa ta zuwa Legas.

A ranar Talata ne Azman ya sanar da dakatar da zirga-zirgar jiragensa zuwa Kaduna har sai baba ta gani saboda rashin tsaro a yankin.

Bayan sa’o’i kadan ne aka samu labarin dakatar da ayyukan jiragen Air Peace zuwa Kaduna.

Karin bayani na nan tafe…

 

 

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp