• Gida
  • DUNIYA
  • Labarai
  • SIYASA
  • TARIHI
  • Taska
  • WASANNI
Search
  • Gida
  • DUNIYA
  • Labarai
  • SIYASA
  • TARIHI
  • Taska
  • WASANNI
Sign in
Welcome! Log into your account
Forgot your password? Get help
Password recovery
Recover your password
A password will be e-mailed to you.
PRNIGERIA PRNigeria Hausa
PRNIGERIA PRNIGERIA
  • Gida
  • DUNIYA
  • Labarai
  • SIYASA
  • TARIHI
  • Taska
  • WASANNI
Home Taska Rundunar ‘Yan Sandan Najeriya ta Kame ‘Yan Kungiyar Asiri Guda 32 a...
  • Taska

Rundunar ‘Yan Sandan Najeriya ta Kame ‘Yan Kungiyar Asiri Guda 32 a Jihar Anambra

By
Prnigeria
-
April 11, 2022
Arewa Award

Rundunar ‘Yan Sandan Najeriya ta Kame ‘Yan Kungiyar Asiri Guda 32 a Jihar Anambra

 

Rundunar ‘Yan Sandan Najeriya reshen jihar Anambra ta sami nasarar kame mutum 32 da take zargi da ayyukan kungiyar Asiri a jihar.

Kakakin Rundunar ‘Yan Sandan jihar DSP Toochukwu Ikenga, ne ya bayyana hakan ta cikin wata sanarwa da ya fitar a ranar lahadi a garin Awka, inda yace dakarun sun sami nasarar bankado bindigu da wasu muggan makamai a hannun wadanda ake zargin.

Mista Ikenga yace samamen da suka kai maboyar ‘yan kungiyar Asirin na matsayin wani bangare na kokarin da hukumar ‘Yan Sandan ke yi na kawar da dukkan nau’in laifuka a jihar.

Ana dai zargin su ne da gudanar da ayyukan Ta’addanci, Fashi da Makami, mallakar makamai ba bisa Ka’ida ba, kamar yadda kakakin ya bayyana.

“A bisa wasu sahihan bayanai, da rundunar ‘Yan Sandan jihar ta samu a ranar 30 ga watan Maris ta sami nasarar kame wani Ozo Olie Ifeanyi, mai kimanin shekaru 43 a gidan sa dake kauyen Odoje a garin Onitsha, inda ta sami karamar bindiga guda daya da kuma Alburushi mai rai guda daya a cikin wata jaka.”

Read Also:

  • Najeriya ce kan gaba a yawan fitar da man fetur a Afirka cikin watan Mayu – OPEC
  • Tinubu zai yi wa ƴan Najeriya jawabi kan ranar dimokuraɗiyya
  • A aƙalla mutum 20 sun rasa rayukansu a saboda hare-hare a Mangu

“sai dai yayi ikirarin cewa shi dan kungiyar Asiri ta Black AX ne, inda yake da kwarewa wajen yin kwace ga wadanda basu ji ba basu gani ba.”

“sannan a wannan rana hukumar ta sami nasarar kame wani da ake zargi, Ifeanyi Nwobu mai kimanin shekaru 49 a duniya dan asalin Enugu-Ukwu”.

“Rundunar ta sami nasarar kwato bindiga kirarar Beretta guda daya, da kuma harsashin guda daya daga hannun wanda ake zargin,” in ji shi.

Mista Ikenga ya kuma ce an kama wasu mutum 30 da ake zargi da aikata laifukan yaki daga shekaru 17 zuwa 44, da laifin karya dokar da gwamnatin jihar Anambra ta hana safara, da kuma karbar kudin haraji ba bisa ka’ida ba.

Yace an damke su ne a ranar 6 ga watan Afrilu a kusa da mahadar Tarzan, daura da kan titin Owerri da hanyar Upper Iweka, da mahadar Ochanja, sai kuma kan hanyar Awada da Head Bridge, da kuma mahadar kara da kan hanyar Atani.

Kakakin rundunar ya nanata kudurin kwamishin ‘yan sandan jihar Anambra, CP Echeng Echeng na kare lafiya da dukiyar al’ummar jihar daga duk wani laifi da rashin tsaro.

“Ba za mu taba yin kasa a gwuiwa ba wajen kare lafiya da dukiyoyin Al’umma, don haka muna kira ga mazauna yankin da su mayar da hankali wajen fallasa dukkanin ayyukan ta’addanci da bata gari ke aikatawa.

PRNigeria Hausa

Kidnapped School Children

Yauri FGC Students, Kebbi
1462 days 9 hours 3 minutes 44 seconds,

Baptist School Students, Kaduna
1444 days 10 hours 45 minutes 9 seconds

Tegina Islamiya Pupils, Niger (Freed)
Spent 88 days from May 30, 2021 - August 26, 2021


Report By: PRNigeria.com

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
  • TAGS
  • 'Yan Sandan Najeriya
  • Anambra
  • Kungiyar Asiri
Previous articleSayen form din takarar gwamna da injinya Magaji Mu’azu yayi yaja cece-kuce
Next article‘Yan Bindiga Sun Kai Hari Birnin Tarayya Abuja
Prnigeria

RELATED ARTICLESMORE FROM AUTHOR

Azumin Bara: Talge Muka Riƙa Sha a Hannun Maharan Jirgin ƙasan Abuja-Kaduna

Zambar N2.2bn: EFCC ta Sake Gurfanar da ɗan Tsohon Shugaban PDP

Magance Karancin Naira: CBN ya Umarci Bankuna da su yi Aiki a Ranakun Asabar da Lahadi

Hatsarin Mota ya yi Sanadiyar Mutuwar Mutane 25 a Bauchi

Hukumar NITDA ta Gabatar da Satifiket ga Matan da Suka Samu Horo Kan Fasahar Zamani

Ambaliyar Ruwa a Jigawa: Gidauniyar Ƙasar Qatar da ta Malam Inuwa Sun Raba Tallafin Abinci ga Mutane 1,000

An Gudanar Da Bikin Arewa Stars 30 Under 30 2022, Cikin Nasara

Manomi Yayiwa Wata Mata Yankan Rago

‘Yan Sanda Sun Kama Wadanda Ake Zargi da Kashe ‘Yan Sanda Biyu a Anambra

Gidauniyar Malam Inuwa Da Kokarinta Na Ilmantar Da Mutanen Karkara Da Rugage

Gidauniyar Malam Inuwa ta Ɗauki Nauyin Koyar da Ƴa’yan Fulani Al-ƙur’ani

Bincike: Shin Hukumar Kidaya ta Kasa (NPC) ta ƙirƙiro da Tambayoyi Domin Tantance kungiyoyin Musulmi da Kirista a kidayar 2023? 

Recent Posts

  • Najeriya ce kan gaba a yawan fitar da man fetur a Afirka cikin watan Mayu – OPEC
  • Tinubu zai yi wa ƴan Najeriya jawabi kan ranar dimokuraɗiyya
  • A aƙalla mutum 20 sun rasa rayukansu a saboda hare-hare a Mangu
  • Najeriya na fuskantar tsaiko kan shirinta na karɓar Dala biliyan 5 daga Saudiya
  • Bom ya kashe masu yawon murnar sallah a Sakkwato

Kidnapped School Children

Yauri FGC Students, Kebbi
1462 days 9 hours 3 minutes 44 seconds,



Baptist School Students, Kaduna
1444 days 10 hours 45 minutes 9 seconds

Report By: prnigeria.com/hausa

Book on Sales: Boko Haram Media War: An Encounter with the Spymaster

boko haram

Click Here:To Order Now!

  • Gida
  • DUNIYA
  • Labarai
  • SIYASA
  • TARIHI
  • Taska
  • WASANNI
© 2020 PRNigeria. All Rights Reserved.
Latest News
Najeriya ce kan gaba a yawan fitar da man fetur a Afirka cikin watan Mayu - OPECTinubu zai yi wa ƴan Najeriya jawabi kan ranar dimokuraɗiyyaA aƙalla mutum 20 sun rasa rayukansu a saboda hare-hare a ManguNajeriya na fuskantar tsaiko kan shirinta na karɓar Dala biliyan 5 daga SaudiyaBom ya kashe masu yawon murnar sallah a SakkwatoNan bada jimawa ba za a samu sauyi a ɓangaren man fetur na Najeriya - DangoteSojojin Najeriya sun kashe ƴan ta’adda 10 a ZamfaraAn samu tashin gobara a masaukin alhazan Najeriya a Shari MansurGwamnatin Neja na yunƙurin haɗa kai da matatar Ɗangote wajen haƙo ɗanyen man feturJirgin sojoji ya kashe ƴan sa-kai a ƙoƙarin fatattakar ƴanbindiga'Hadarin mota ya yi sanadiyyar matasa 22 'yan asalin KanoGwamnatin Tinubu ta jefa ƴan Najeriya fiye da miliyan 150 cikin tsananin talauci - NLCSojoji sun ce sun hallaka ƴan ta'adda 60 a jihar BornoAn kama mutane 41 kan zargin kashe DPO a KanoRayuwar ƴan Najeriya na ƙara inganta - Tinubu
X whatsapp