Home SIYASA Yanzu – Yanzu: Karin Kwamishinoni Sun yi Murabus a Jihar Kano

Yanzu – Yanzu: Karin Kwamishinoni Sun yi Murabus a Jihar Kano

Wasu Karin Kwamishinonin da Mataimaki na musamman ga Gwamnan Jihar Kano Dakta Abdullahi Umar Ganduje da suka hadar da Kwamishinan Ilimi na Jihar Kano, Sunusi Sa’idu Kiru da babban mataimaki na musamman ga Gwamnan jihar kano Faruq Sule Garo sun yi murabus daga mukaman su.

Ta cikin takardar Murabus da kwamishinan Ilimin Sunusi Sa’idu Kiru ya aiki wa gwamnan, ya gode masa matuka bisa damar da ya bashi na yiwa al’umma aiki a karkashin gwamnatin sa.

Ganduje ya bayar da umarni ga dukkan masu Muradin tsayawa Takara a cikin jami’an Gwamnatin Jihar Kano suyi murabus daga nan zuwa  ranar litinin. Umarnin da yayi daidai da sashe na 84(12) na sabuwar dokar zabe da aka yiwa gyaran fuska.

Tuni dai wasu kwamishinoni uku daga cikin kwamishinonin kunshin gwamantin Jihar Kano suka sanar da ajje aikin nasu, ta cikin takaddun sanarwa da suka aike ga Gwamnan.

Kwamishinonin sun hadar da Kwamishinan Kananan Hukumomi Murtala Sule Garo, Kwamishinan Karkara Musa Iliyasu Kwankwaso da na Kasafi da Tsare Tsare Nura Dankadai.

Sunusi Kiru ya bayyana Murabus din nashi matsayin abinda zai bashi damar wakiltar Bebeji/Kiru a Zauren Majalisar Wakilan Nijeriya.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp