Home SIYASA Yanzu – Yanzu: Karin Kwamishinoni Sun yi Murabus a Jihar Kano

Yanzu – Yanzu: Karin Kwamishinoni Sun yi Murabus a Jihar Kano

Wasu Karin Kwamishinonin da Mataimaki na musamman ga Gwamnan Jihar Kano Dakta Abdullahi Umar Ganduje da suka hadar da Kwamishinan Ilimi na Jihar Kano, Sunusi Sa’idu Kiru da babban mataimaki na musamman ga Gwamnan jihar kano Faruq Sule Garo sun yi murabus daga mukaman su.

Ta cikin takardar Murabus da kwamishinan Ilimin Sunusi Sa’idu Kiru ya aiki wa gwamnan, ya gode masa matuka bisa damar da ya bashi na yiwa al’umma aiki a karkashin gwamnatin sa.

Ganduje ya bayar da umarni ga dukkan masu Muradin tsayawa Takara a cikin jami’an Gwamnatin Jihar Kano suyi murabus daga nan zuwa  ranar litinin. Umarnin da yayi daidai da sashe na 84(12) na sabuwar dokar zabe da aka yiwa gyaran fuska.

Tuni dai wasu kwamishinoni uku daga cikin kwamishinonin kunshin gwamantin Jihar Kano suka sanar da ajje aikin nasu, ta cikin takaddun sanarwa da suka aike ga Gwamnan.

Kwamishinonin sun hadar da Kwamishinan Kananan Hukumomi Murtala Sule Garo, Kwamishinan Karkara Musa Iliyasu Kwankwaso da na Kasafi da Tsare Tsare Nura Dankadai.

Sunusi Kiru ya bayyana Murabus din nashi matsayin abinda zai bashi damar wakiltar Bebeji/Kiru a Zauren Majalisar Wakilan Nijeriya.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Shin AtikuObi Zasu Iya Tsige TinubuShettima a 2027? Daga Yushau A. ShuaibYadda Shari'ar Masarautar Kano ke Ci gaba da Wakana a Kotun ta ƙoliTawagar Amurka na Shirin Tafiya Pakistan Domin Tattaunawar Sulhu da IranDole Najeriya ta Samu Tsaro ta Kowane Hali - Babban Hafsan TsaroChelsea da Newcastle na Harin Coulibaly, Liverpool na Neman Siyan Marcos SensiBadaƙalar $1.3m: Kotu ta ba EFCC izinin Kama Tsohuwar Ministar jin ƙan Najeriya Sadiya FarouqRaphinha ya Magantu kan Fitar da ƙungiyarsa da aka yi Daga Champion LigRundunar sojin Najeriya ta Musanta bai wa Tsofaffin Mayaƙan Boko Haram MakamaiGwamnatin Tarayya ta Sauya Zarge-Zargen da ta ke yi wa MalamiAn Binne Birgediya Janar Braimah da Sauran Sojojin da Boko Haram ta KasheYaƙin Iran: Hauhawar farashin Kaya a Najeriya ya ƙaruAdadin Matasa 'Yan kwaya da Muka Kama a Shekara 5 - NDLEAJam'iyyar ADC ta Kori Nafi'u Bala GombeRigakafin ƙyanda ya Ceci Yara Miliyan 20 a Afirka - Hukumar Lafiya ta Duniya2027 Ita ce Dama ta ƙarshe da zan Fito Takara - Atiku
X whatsapp