Home SIYASA Yanzu – Yanzu: Karin Kwamishinoni Sun yi Murabus a Jihar Kano

Yanzu – Yanzu: Karin Kwamishinoni Sun yi Murabus a Jihar Kano

Wasu Karin Kwamishinonin da Mataimaki na musamman ga Gwamnan Jihar Kano Dakta Abdullahi Umar Ganduje da suka hadar da Kwamishinan Ilimi na Jihar Kano, Sunusi Sa’idu Kiru da babban mataimaki na musamman ga Gwamnan jihar kano Faruq Sule Garo sun yi murabus daga mukaman su.

Ta cikin takardar Murabus da kwamishinan Ilimin Sunusi Sa’idu Kiru ya aiki wa gwamnan, ya gode masa matuka bisa damar da ya bashi na yiwa al’umma aiki a karkashin gwamnatin sa.

Ganduje ya bayar da umarni ga dukkan masu Muradin tsayawa Takara a cikin jami’an Gwamnatin Jihar Kano suyi murabus daga nan zuwa  ranar litinin. Umarnin da yayi daidai da sashe na 84(12) na sabuwar dokar zabe da aka yiwa gyaran fuska.

Tuni dai wasu kwamishinoni uku daga cikin kwamishinonin kunshin gwamantin Jihar Kano suka sanar da ajje aikin nasu, ta cikin takaddun sanarwa da suka aike ga Gwamnan.

Kwamishinonin sun hadar da Kwamishinan Kananan Hukumomi Murtala Sule Garo, Kwamishinan Karkara Musa Iliyasu Kwankwaso da na Kasafi da Tsare Tsare Nura Dankadai.

Sunusi Kiru ya bayyana Murabus din nashi matsayin abinda zai bashi damar wakiltar Bebeji/Kiru a Zauren Majalisar Wakilan Nijeriya.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mayaƙan Lakurawa Sun Kashe Sojoji 7 a SokotoAn faɗa wa Shugaba Tinubu Cewa Ina Kitsa Yadda Zan Kashe Shi - ShettimaRundunar 'Yan Sandan Najeriya ta Ceto ƴan Mali 30 Daga Hannun Masu Safarar MutaneMun Kashe Mayaƙan ISIS 175 - Rundunar Sojin NajeriyaFarfesa Pantami ya Janye Daga Takarar Gwamnan Jihar GombeKishiya: Tsakanin ONSA na Ribadu da Tsaron Gida Famadewa Daga Yushau A. ShuaibZaben Fidda Gwani: An Harbe Mutum a Jihar PlateauRundunar 'Yan Sanda ta Tabbatar Kashe Jami'anta 17 a YobeSatar Kayayyakin Banki: An Kama Mutane Huɗu a Jihar Gombe'Yan Bindiga Sun Sace Basarake Tare da Mata 2 a KatsinaJami'an Kwastam Biyu sun Rasa Ransu a Fafatawa da LakurawaMatar Aure ta Zuba wa Kishiyarta da 'Ya'yanta Biyu Fetur Tare da Banka Musu Wuta a KanoIna da ƴancin Mu'amala da Kowa ba Tare da La'akari da Jam'iyya ba - WikeAdadin Masu Fama da Cutar Tamowa na ƙaruwa a Najeriya - MSFGwamnatin Yobe ta Sha Alwashin Kawo ƙarshen Hare-Haren Boko Haram
X whatsapp