Home General Mayakan ISWAP Sun mika wuya a Jamhuriyyar Nijar

Mayakan ISWAP Sun mika wuya a Jamhuriyyar Nijar

Mayajan kungiyar tada kayar Baya na ISWAP da suka tsallake rijiya da baya, bayab harin da tsagin Boko Haram ya kai mu a Kayowa da Toumbun Gini, a Arewa maso gabshin yankin Tafkin Chadi, sun mika wuya hannun hukumomi a Tumour, ta Jamhuriyyar Nijar.
Zagazola ya ruwaito cewa mayakan ISWAP sun mika wuya a ranar 10 ga watan Janairu biyo bayan harin da abokan hamayyar su ta boko haram ke kai musu.

Harin ISWAP kan sansanin boko haram ya haifar da asarar rayuka tun a ranakun 31 ga Disamba da kuma 8 ga watan Janairun, 2023.
Harin kungiyar ta kai bisa jagorancin ABU UMAIMAH da akafi sanj da BAKOURA DORO, ya tarwatsa maboyar yan Ta’addan dake Toumbum Allura, Kurnawa, Kayowa da kuma Toumbun Gini, wanda ya tilastawa Abu Moussab al-Barnawi da wasu kwamandojin tsirewa.

Ci gaba da fafatawa tsakanin JAS da ISWAP dai da alama dai ba mai karewa ba ce ganin yadda yunkurin da kungiyoyin ke yi na hada karfi da karfe domin yakar sojojin Najeriya da na MNJTF ya gagara.

Dangane da wannan yanayin ne kungiyar ISWAP ke neman goyon bayan mayakan ISIS na kasashen waje da suka hadar da Mali, Burkina Faso da Somaliya don taimaka musu su karya JAS.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mayaƙan Lakurawa Sun Kashe Sojoji 7 a SokotoAn faɗa wa Shugaba Tinubu Cewa Ina Kitsa Yadda Zan Kashe Shi - ShettimaRundunar 'Yan Sandan Najeriya ta Ceto ƴan Mali 30 Daga Hannun Masu Safarar MutaneMun Kashe Mayaƙan ISIS 175 - Rundunar Sojin NajeriyaFarfesa Pantami ya Janye Daga Takarar Gwamnan Jihar GombeKishiya: Tsakanin ONSA na Ribadu da Tsaron Gida Famadewa Daga Yushau A. ShuaibZaben Fidda Gwani: An Harbe Mutum a Jihar PlateauRundunar 'Yan Sanda ta Tabbatar Kashe Jami'anta 17 a YobeSatar Kayayyakin Banki: An Kama Mutane Huɗu a Jihar Gombe'Yan Bindiga Sun Sace Basarake Tare da Mata 2 a KatsinaJami'an Kwastam Biyu sun Rasa Ransu a Fafatawa da LakurawaMatar Aure ta Zuba wa Kishiyarta da 'Ya'yanta Biyu Fetur Tare da Banka Musu Wuta a KanoIna da ƴancin Mu'amala da Kowa ba Tare da La'akari da Jam'iyya ba - WikeAdadin Masu Fama da Cutar Tamowa na ƙaruwa a Najeriya - MSFGwamnatin Yobe ta Sha Alwashin Kawo ƙarshen Hare-Haren Boko Haram
X whatsapp