Home General Mayakan ISWAP Sun mika wuya a Jamhuriyyar Nijar

Mayakan ISWAP Sun mika wuya a Jamhuriyyar Nijar

Mayajan kungiyar tada kayar Baya na ISWAP da suka tsallake rijiya da baya, bayab harin da tsagin Boko Haram ya kai mu a Kayowa da Toumbun Gini, a Arewa maso gabshin yankin Tafkin Chadi, sun mika wuya hannun hukumomi a Tumour, ta Jamhuriyyar Nijar.
Zagazola ya ruwaito cewa mayakan ISWAP sun mika wuya a ranar 10 ga watan Janairu biyo bayan harin da abokan hamayyar su ta boko haram ke kai musu.

Harin ISWAP kan sansanin boko haram ya haifar da asarar rayuka tun a ranakun 31 ga Disamba da kuma 8 ga watan Janairun, 2023.
Harin kungiyar ta kai bisa jagorancin ABU UMAIMAH da akafi sanj da BAKOURA DORO, ya tarwatsa maboyar yan Ta’addan dake Toumbum Allura, Kurnawa, Kayowa da kuma Toumbun Gini, wanda ya tilastawa Abu Moussab al-Barnawi da wasu kwamandojin tsirewa.

Ci gaba da fafatawa tsakanin JAS da ISWAP dai da alama dai ba mai karewa ba ce ganin yadda yunkurin da kungiyoyin ke yi na hada karfi da karfe domin yakar sojojin Najeriya da na MNJTF ya gagara.

Dangane da wannan yanayin ne kungiyar ISWAP ke neman goyon bayan mayakan ISIS na kasashen waje da suka hadar da Mali, Burkina Faso da Somaliya don taimaka musu su karya JAS.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 6 Sun Rasu 4 Sun Jilkata Sanadiyyar Tsawa a Jihar AdamawaMatatar Dangote ta Dakatar da Amfani da Naira Wajen Sayar da Man FeturZaɓen 2027: Jam'iyyar ADC ta Mayar da Martani kan Hukuncin Kotu Akwai Yiwuwar ba zan kai Lokacin Zaɓen 2027 ba - ObiHukuncin da Kotu ta Yanke wa Direban Keke Napep Kan Aikata Fyaɗeɓata Sunan Gwamnatin Katsina: Kotu ta buƙaci Ƴan Sanda su Tsare Dr Kurfi Gwamnonin Arewacin Najeriya sun Kafa Gidauniyar Yaƙi da Matsalar TsaroGwamnatin Tarayya ba ta Yanke Hukuncin Sauya Kayan NYSC ba - Ministan MatasaJuyin Mulki: DSS ta Gurfanar da Mutane 5 kan ɓoye Timipre Sylva Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 2 Tare da Limami a Jihar Sokoto Dakarun Soji Sun Bankaɗo Wajen ƙera da Rarraba Bindigogi ga Ƴan Ta'addaJami'an DSS Sun Kama Tsohon Ministan Kimiyya da Fasaha, Uche NnajiYan Bindiga Sun Hallaka Mutane 10 a Jihar BenueNMDPRA ta Gargaɗi Gidajen Man da ba su Rage Farashi ba NECO: ɗalibai 35 na Hannun Ƴan Bindiga - Ƴan Sanda 
X whatsapp