Home General Yara sama da miliyan 30 na fuskantar Barazanar Yunwa a sassan Duniya

Yara sama da miliyan 30 na fuskantar Barazanar Yunwa a sassan Duniya

Majalisar Dinkin Duniya ta bukaci daukar matakan gaggawa don ceto yara fiye da miliyan 30 da ke fuskantar barazanar cutar yunwa a kasashe 15 da ke fama da matsananciyar yunwa ciki har da Najeria Sanarwar wadda sassan lafiya da abinci da kuma kula da kananan yara na Majalisar Dinkin Duniya 5 suka fitar sun yi gargadin cewa matukar ba a dauki matakan da suka kamata ba, ko shakka babu yaran fiye da miliyan 30 za su fuskanci cutar yunwa sakamakon rashin abinci mai gina jiki.

Sanarwar ta Majalisar Dinkin Duniya da ke wannan gargadi ta zayyano kasashen da za su fuskanci wannan matsala ciki har da Afghanistan da Burkina Faso da Chadi da Jamhuriyyar Demokradiyyar Congo baya ga Habasha da Haiti da Kenya da kuma Madagascar sai kasashen Mali, Nijar, Najeriya da Somalia da Sudan ta kudu kana Sudan da Yemen.

Sassan na Majalisar 5 da suka kunshi hukumar abinci ta duniya FAO da mai kula da bakin haure UNHCR da kuma asusun tallafawa kananan yara na UNICEF da WHO baya ga shirin samar da abinci na duniya WFP sun ce wajibi ne a hada hannu don hana faruwar wannan annoba da ke tunkaro Duniya.

A cewar sanarwar sassan 5 cutar ta yunwa ko kuma rashin abincin mai gina jiki ga kananan yara na sahun cutukan da ke haddasa asarar rayukan miliyoyin yara kowacce shekara musamman a matalautan kasashe ko kuma wadanda yaki ko matsalar tsaro ta daidaita.

Sassan Majalisar sun bayyana cewa wajibi ne Duniya ta mike tsaye don tunkarar matsalar da nufin ceto yaran fiye da miliyan 30 wadanda rayuwarsu ke halin tsaka mai wuya saboda karanci ko kuma rashin abincin mai gina jiki baki daya.

PRNigeria hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp