Home General Yara sama da miliyan 30 na fuskantar Barazanar Yunwa a sassan Duniya

Yara sama da miliyan 30 na fuskantar Barazanar Yunwa a sassan Duniya

Majalisar Dinkin Duniya ta bukaci daukar matakan gaggawa don ceto yara fiye da miliyan 30 da ke fuskantar barazanar cutar yunwa a kasashe 15 da ke fama da matsananciyar yunwa ciki har da Najeria Sanarwar wadda sassan lafiya da abinci da kuma kula da kananan yara na Majalisar Dinkin Duniya 5 suka fitar sun yi gargadin cewa matukar ba a dauki matakan da suka kamata ba, ko shakka babu yaran fiye da miliyan 30 za su fuskanci cutar yunwa sakamakon rashin abinci mai gina jiki.

Sanarwar ta Majalisar Dinkin Duniya da ke wannan gargadi ta zayyano kasashen da za su fuskanci wannan matsala ciki har da Afghanistan da Burkina Faso da Chadi da Jamhuriyyar Demokradiyyar Congo baya ga Habasha da Haiti da Kenya da kuma Madagascar sai kasashen Mali, Nijar, Najeriya da Somalia da Sudan ta kudu kana Sudan da Yemen.

Sassan na Majalisar 5 da suka kunshi hukumar abinci ta duniya FAO da mai kula da bakin haure UNHCR da kuma asusun tallafawa kananan yara na UNICEF da WHO baya ga shirin samar da abinci na duniya WFP sun ce wajibi ne a hada hannu don hana faruwar wannan annoba da ke tunkaro Duniya.

A cewar sanarwar sassan 5 cutar ta yunwa ko kuma rashin abincin mai gina jiki ga kananan yara na sahun cutukan da ke haddasa asarar rayukan miliyoyin yara kowacce shekara musamman a matalautan kasashe ko kuma wadanda yaki ko matsalar tsaro ta daidaita.

Sassan Majalisar sun bayyana cewa wajibi ne Duniya ta mike tsaye don tunkarar matsalar da nufin ceto yaran fiye da miliyan 30 wadanda rayuwarsu ke halin tsaka mai wuya saboda karanci ko kuma rashin abincin mai gina jiki baki daya.

PRNigeria hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 6 Sun Rasu 4 Sun Jilkata Sanadiyyar Tsawa a Jihar AdamawaMatatar Dangote ta Dakatar da Amfani da Naira Wajen Sayar da Man FeturZaɓen 2027: Jam'iyyar ADC ta Mayar da Martani kan Hukuncin Kotu Akwai Yiwuwar ba zan kai Lokacin Zaɓen 2027 ba - ObiHukuncin da Kotu ta Yanke wa Direban Keke Napep Kan Aikata Fyaɗeɓata Sunan Gwamnatin Katsina: Kotu ta buƙaci Ƴan Sanda su Tsare Dr Kurfi Gwamnonin Arewacin Najeriya sun Kafa Gidauniyar Yaƙi da Matsalar TsaroGwamnatin Tarayya ba ta Yanke Hukuncin Sauya Kayan NYSC ba - Ministan MatasaJuyin Mulki: DSS ta Gurfanar da Mutane 5 kan ɓoye Timipre Sylva Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 2 Tare da Limami a Jihar Sokoto Dakarun Soji Sun Bankaɗo Wajen ƙera da Rarraba Bindigogi ga Ƴan Ta'addaJami'an DSS Sun Kama Tsohon Ministan Kimiyya da Fasaha, Uche NnajiYan Bindiga Sun Hallaka Mutane 10 a Jihar BenueNMDPRA ta Gargaɗi Gidajen Man da ba su Rage Farashi ba NECO: ɗalibai 35 na Hannun Ƴan Bindiga - Ƴan Sanda 
X whatsapp