Home General An sanya dokar hana fita a Jihar Niger

An sanya dokar hana fita a Jihar Niger

Gwamnatin jihar Niger ta sanya dokar ta baci biyo bayan kisan wani mai gari a jihar.
Gwamnan jihar Niger Abubakar Sani Bello ya sanay dokar hana zirga-zirga a kauyen
Lambata dake karamar hukumar Gurara, biyo bayan wata hatsaniya da tayi sanadiyyar hallaka wani mai rike da sarautar gargaji Mohammed Abdulsafur.
Wannan na kunshe ne ta cikin wata sanarwa da sakataren Gwamnati jihar Ahmed Matane, ya fitar a ranar lahadi a Minna babban birnin jihar.
Rahotanni sun bayyana cewa ‘yan daba sun hallaka dagacin Lamabata ne a ranar Asabar biyo bayan wata tarzoma.
Bello ya bada umarnin cewa

Dokar zata fara ne daga karfe 6:00am Zuwa 6:oopm farawa daga ranar Lahadi kuma har sai baba ta gani.
Ya kara da cewa an sanya dokar ne domin taimakawa jami’an tsaro su nemo bakin zaren matsalar, su tseratar da Rayukan Al’umma da dawo da doka da Odar.
Sanarwa ta kuma bayyana cewa Gwamnatin jihar tayi Allawadai da wannan tarzoma data auku a garin na lambata.
Ta kuma bukaci Al’ummar garin dasu bi doka domin baya jami’an tsaro damar dawo da zaman lafiya a garin.

PRNigeria hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 200 Sun Mutu Sakomakon Girgizar ƙasar a ColombiaShahararren Mawaƙin Najeriya, Davido ya Rubuta wa Trump Wasiƙa Kan Zaɓen Jihar OsunHukumar NHRC ta Buƙaci a Kama Malamin Addinin, Sheikh JingirRundunar sojin Najeriya ta Daƙile Shirin Ƴan Bindiga a FilatoJami'an Ƴan Sanda 10 Sun Mutu Yayin Artabu da Ƴan Bindiga a Jihar KebbiAn Naɗa ɗan Najeriya Gidado Shuaib Wakilin Matasa na IPRA-UN Gabanin GWAEFCC da "Wuce Gona da Iri" da Tambayar 2027: Shin ana Rudar da Tinubu ta Hanyar Mutanen da ke Kewaye da Shi ? Daga Yushau A. ShuaibAn Samu Gawar Yara 3 da guda 1 a Sume a Gidan Mai Maganin GargajiyaMene ne Ainihin Abin da ya faru Aka Rufe Asusun Bankunan Gwamnatin Osun ?Jami'an Tsaro Sun Ceto Mutane 308 a Jihohin Arewacin Najeriya An Kama Mutane 6 da Ake Zargin da Taimaka wa Mayaƙan ISWAP a Jihar BornoZaɓen 2027: PDP ta Miƙa Sunan Jonathan ga INEC a Matsayin ɗan Takararta na Shugaban ƙasaIyanen Babban Jami'in Kula da Harkokin Kuɗaɗen ƙungiyar ISWAP Sun Miƙa Wuya ga SojojiAna Zargin Mayaƙan Boko Haram da Kashe Sojojin Nijar 14Gombe 2027: Malamai da Mambobin APC Sun yi Allah-wadai da Sukar Rarara ga Pantami
X whatsapp