Home General An sanya dokar hana fita a Jihar Niger

An sanya dokar hana fita a Jihar Niger

Gwamnatin jihar Niger ta sanya dokar ta baci biyo bayan kisan wani mai gari a jihar.
Gwamnan jihar Niger Abubakar Sani Bello ya sanay dokar hana zirga-zirga a kauyen
Lambata dake karamar hukumar Gurara, biyo bayan wata hatsaniya da tayi sanadiyyar hallaka wani mai rike da sarautar gargaji Mohammed Abdulsafur.
Wannan na kunshe ne ta cikin wata sanarwa da sakataren Gwamnati jihar Ahmed Matane, ya fitar a ranar lahadi a Minna babban birnin jihar.
Rahotanni sun bayyana cewa ‘yan daba sun hallaka dagacin Lamabata ne a ranar Asabar biyo bayan wata tarzoma.
Bello ya bada umarnin cewa

Dokar zata fara ne daga karfe 6:00am Zuwa 6:oopm farawa daga ranar Lahadi kuma har sai baba ta gani.
Ya kara da cewa an sanya dokar ne domin taimakawa jami’an tsaro su nemo bakin zaren matsalar, su tseratar da Rayukan Al’umma da dawo da doka da Odar.
Sanarwa ta kuma bayyana cewa Gwamnatin jihar tayi Allawadai da wannan tarzoma data auku a garin na lambata.
Ta kuma bukaci Al’ummar garin dasu bi doka domin baya jami’an tsaro damar dawo da zaman lafiya a garin.

PRNigeria hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp