Home General ‘Yan Nijeriya miliyan 25 ka iya fuskantar matsalar Yunwa a cikin shekarar...

‘Yan Nijeriya miliyan 25 ka iya fuskantar matsalar Yunwa a cikin shekarar 2023

Wani rahoto da aka fitar ya nuna cewa ‘yan Najeriya miliyan 25 na cikin barazanar faɗawa halin yunwa tsakanin watan Yuni da kuma Agustan 2023 muddin ba a dauki matakin gaggawa ba.

Rahoton wanda kungiyar Cadre Harmonisé ta fitar, wadda kungiya ce ta Majalisar Dinkin Duniya da ke taimakawa wajen samar da abinci mai gina jiki, ya nuna cewa ƙasar na ci gaba da fama da rikice-rikice da sauyin yanayi da kuma hauhawar farashin kayan abinci.

A cewar wata sanarwa ta haɗin gwiwa da hukumar noma da samar da abinci da asusun kula da yara na Majalisar Dinkin Duniya da hukumar bayar da agaji suka fitar, ta ce hakan ya nuna ƙaruwa a mutane miliyan 17 da ke fama da matsalar ƙarancin abinci a yanzu.

Sanarwar ta kuma lura cewa an ayyukan ‘yan ta-da-ƙayar-baya ya shafi aikin samar da abinci a yankin arewa maso gabas da suka hadar da jihohin Borno, Adamawa da kuma Yobe da kuma matsalar ayyukan ‘yan bindiga da garkuwa da mutane a Katsina da Sokoto da Kaduna da Benue da kuma Neja.

Sanarwar ta ce Hukumar Bayar da Agajin Gaggawa ta Ƙasa NEMA, ta ruwaito cewa matsalar ambaliyar ruwa da aka samu a shekarar 2022, ya lalata kadada 676,000 na gonaki wanda kuma ya kawo raguwa a abin da mutane suka girba da janyo ƙaruwar barazanar matsalar ƙarancin abinci ga iyalai a faɗin kasar

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Shin AtikuObi Zasu Iya Tsige TinubuShettima a 2027? Daga Yushau A. ShuaibYadda Shari'ar Masarautar Kano ke Ci gaba da Wakana a Kotun ta ƙoliTawagar Amurka na Shirin Tafiya Pakistan Domin Tattaunawar Sulhu da IranDole Najeriya ta Samu Tsaro ta Kowane Hali - Babban Hafsan TsaroChelsea da Newcastle na Harin Coulibaly, Liverpool na Neman Siyan Marcos SensiBadaƙalar $1.3m: Kotu ta ba EFCC izinin Kama Tsohuwar Ministar jin ƙan Najeriya Sadiya FarouqRaphinha ya Magantu kan Fitar da ƙungiyarsa da aka yi Daga Champion LigRundunar sojin Najeriya ta Musanta bai wa Tsofaffin Mayaƙan Boko Haram MakamaiGwamnatin Tarayya ta Sauya Zarge-Zargen da ta ke yi wa MalamiAn Binne Birgediya Janar Braimah da Sauran Sojojin da Boko Haram ta KasheYaƙin Iran: Hauhawar farashin Kaya a Najeriya ya ƙaruAdadin Matasa 'Yan kwaya da Muka Kama a Shekara 5 - NDLEAJam'iyyar ADC ta Kori Nafi'u Bala GombeRigakafin ƙyanda ya Ceci Yara Miliyan 20 a Afirka - Hukumar Lafiya ta Duniya2027 Ita ce Dama ta ƙarshe da zan Fito Takara - Atiku
X whatsapp