Home General Zargin sayar da Man Fetur Ba bisa ka’ida ba ya haddasa Gobara...

Zargin sayar da Man Fetur Ba bisa ka’ida ba ya haddasa Gobara a Gidan Man NNPCL Na Jihar Kano

Zargin sayar da man fetur ba bisa ka’ida bay a haddasa tashin wata gobara a gidan mai mallakin kamfanin NNPCL dake shatale-talen kano Club dake jihar kano a Arewa maso yammacin Nijeriya.
Wannan dai iftila’I na zuwa ne daidai lokacin da Al’umma jihar da wasu jihohihin dake kasar ke fama da matsalar karanci da tsadar manfetur sakamakon rashin tartibin farashin sa.
Shaidun gani da ido sun tabbatar wa da PRNigeria cewa bayan kammala zuba man ne a wata mota kirar Sienna wadda aka yi mata Karin tanki ne lamarin ya auku.
Sai dai duk da kokarin hukumar kashe gobara na dakile yaduwar gobarar lamarin sai da ya kai ga konewar motar kurmus.
Wani shaida ma da lamarin ya faru gaban idon sa wanda ya bukaci a sakaye sunan  sa sakamakon alaka da yake da ita da gidan man yace, ana tsaka da zuba man ne hukumomin gidan man suka hangi hukumar tsaro ta farin kaya dake yawo domin ganin an sayar da man yadda yake a farashin da gwamnati ta bayar, nan ne a kokarin su na gaggauta boyewa wutar ta tashi a motar.

Ba wannan ne karon farko da gobara ke tashi a gidajen man dake jihar kano ba sai dai a iya cewa wannan yazo da sauki domin kawo yanzu babu wani rahoton asarar rayuka sakamakon gobarar.

PRNigeria hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp