Home General Zargin sayar da Man Fetur Ba bisa ka’ida ba ya haddasa Gobara...

Zargin sayar da Man Fetur Ba bisa ka’ida ba ya haddasa Gobara a Gidan Man NNPCL Na Jihar Kano

Zargin sayar da man fetur ba bisa ka’ida bay a haddasa tashin wata gobara a gidan mai mallakin kamfanin NNPCL dake shatale-talen kano Club dake jihar kano a Arewa maso yammacin Nijeriya.
Wannan dai iftila’I na zuwa ne daidai lokacin da Al’umma jihar da wasu jihohihin dake kasar ke fama da matsalar karanci da tsadar manfetur sakamakon rashin tartibin farashin sa.
Shaidun gani da ido sun tabbatar wa da PRNigeria cewa bayan kammala zuba man ne a wata mota kirar Sienna wadda aka yi mata Karin tanki ne lamarin ya auku.
Sai dai duk da kokarin hukumar kashe gobara na dakile yaduwar gobarar lamarin sai da ya kai ga konewar motar kurmus.
Wani shaida ma da lamarin ya faru gaban idon sa wanda ya bukaci a sakaye sunan  sa sakamakon alaka da yake da ita da gidan man yace, ana tsaka da zuba man ne hukumomin gidan man suka hangi hukumar tsaro ta farin kaya dake yawo domin ganin an sayar da man yadda yake a farashin da gwamnati ta bayar, nan ne a kokarin su na gaggauta boyewa wutar ta tashi a motar.

Ba wannan ne karon farko da gobara ke tashi a gidajen man dake jihar kano ba sai dai a iya cewa wannan yazo da sauki domin kawo yanzu babu wani rahoton asarar rayuka sakamakon gobarar.

PRNigeria hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 6 Sun Rasu 4 Sun Jilkata Sanadiyyar Tsawa a Jihar AdamawaMatatar Dangote ta Dakatar da Amfani da Naira Wajen Sayar da Man FeturZaɓen 2027: Jam'iyyar ADC ta Mayar da Martani kan Hukuncin Kotu Akwai Yiwuwar ba zan kai Lokacin Zaɓen 2027 ba - ObiHukuncin da Kotu ta Yanke wa Direban Keke Napep Kan Aikata Fyaɗeɓata Sunan Gwamnatin Katsina: Kotu ta buƙaci Ƴan Sanda su Tsare Dr Kurfi Gwamnonin Arewacin Najeriya sun Kafa Gidauniyar Yaƙi da Matsalar TsaroGwamnatin Tarayya ba ta Yanke Hukuncin Sauya Kayan NYSC ba - Ministan MatasaJuyin Mulki: DSS ta Gurfanar da Mutane 5 kan ɓoye Timipre Sylva Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 2 Tare da Limami a Jihar Sokoto Dakarun Soji Sun Bankaɗo Wajen ƙera da Rarraba Bindigogi ga Ƴan Ta'addaJami'an DSS Sun Kama Tsohon Ministan Kimiyya da Fasaha, Uche NnajiYan Bindiga Sun Hallaka Mutane 10 a Jihar BenueNMDPRA ta Gargaɗi Gidajen Man da ba su Rage Farashi ba NECO: ɗalibai 35 na Hannun Ƴan Bindiga - Ƴan Sanda 
X whatsapp