Home General Shugaban hukumar NUC ya Kaddamar da Tagwayen dakunan daukar Darasi a Jami’ar...

Shugaban hukumar NUC ya Kaddamar da Tagwayen dakunan daukar Darasi a Jami’ar MAUUN Dake Kano.

Babban Sakataren hukumar dake lura da Jami’oi a Nijeriya NUC Farfesa Abubakar Adamu Rasheed a ranar Litinin ya kaddamar da tagwayen dakunan daukar darasi wanda aka sanya sunan sa a jami’ar Maryam Abacha American University ta Nigeria (MAAUN), Kano.
Farfesa Rasheed a yayin da yake kaddamar da ginin, ya bayyana gasuwarsa da irin kayayyakin da aka zuba a cikin ta, ya kuma godewa hukumar gudanarwar Jami’ar bisa sanya mata sunan sa da tayi.
Ya kuma yaba da gudunmawar farfesa Adamu Abubakar Gwarzo na daga darajar fannin ilimi a Nijeriya da sauran kasashe.
Farfesa Rasheed ya sami damar zagayawa wasu gine-gine a cikin Jami’ar da suka hadar da dakin karatu na Murtala Ramat, filin wasa na Mohammed Ibrahim Usman Yakasai da dai sauransu.
Yayin ziyarar Farfesa Rasheed ya sami tarbar farfesa Prof. Gwarzo, Matainakin shugaba Jami’ar a fanni Gudanarwa Dr. Habib Awais Abubakar, sai mataimaki na fannin harkokin Jami’ar da walwalar dalibai Dr. Hamza Garba and Prof. Ibrahim Usman Yakasai.
Da dai sauran shuwagabanni sashe daban-daban na Jami’ar ta MAUUN dake jihar Kano.

PRNigeria hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 6 Sun Rasu 4 Sun Jilkata Sanadiyyar Tsawa a Jihar AdamawaMatatar Dangote ta Dakatar da Amfani da Naira Wajen Sayar da Man FeturZaɓen 2027: Jam'iyyar ADC ta Mayar da Martani kan Hukuncin Kotu Akwai Yiwuwar ba zan kai Lokacin Zaɓen 2027 ba - ObiHukuncin da Kotu ta Yanke wa Direban Keke Napep Kan Aikata Fyaɗeɓata Sunan Gwamnatin Katsina: Kotu ta buƙaci Ƴan Sanda su Tsare Dr Kurfi Gwamnonin Arewacin Najeriya sun Kafa Gidauniyar Yaƙi da Matsalar TsaroGwamnatin Tarayya ba ta Yanke Hukuncin Sauya Kayan NYSC ba - Ministan MatasaJuyin Mulki: DSS ta Gurfanar da Mutane 5 kan ɓoye Timipre Sylva Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 2 Tare da Limami a Jihar Sokoto Dakarun Soji Sun Bankaɗo Wajen ƙera da Rarraba Bindigogi ga Ƴan Ta'addaJami'an DSS Sun Kama Tsohon Ministan Kimiyya da Fasaha, Uche NnajiYan Bindiga Sun Hallaka Mutane 10 a Jihar BenueNMDPRA ta Gargaɗi Gidajen Man da ba su Rage Farashi ba NECO: ɗalibai 35 na Hannun Ƴan Bindiga - Ƴan Sanda 
X whatsapp