Home General NDLEA Ta kama Hodar Iblis da aka shigar da ita Nijeriya daga...

NDLEA Ta kama Hodar Iblis da aka shigar da ita Nijeriya daga Brazil da Canada

Hukumar da ke Hana Sha da Fataucin miyagun kwayoyi ta Najeriya NDLEA ta ce ta samu nasarar kama hodar ibilis da tabar wiwi da aka shiga ƙasar da ita daga ƙasashen Brazil da Canada a biranen Enugu da Legas.

Wannan na kunshe ta cikin wata sanarwa da jami’in hulda da jama’a na hukumar Femi Babafemi ya sanya wa hannu, inda tace ce hukumar ta kama ƙwayoyin tramadol miliyan 1.7 a birnin Legas da ke kudu maso yammacin ƙasar, tare da kama mutanen da ta daɗe tana nema a jihohin Osun da Kano da Ondo da Edo da Abuja babban birnin ƙasar.

Sanarwar ta ci gaba da cewa ”Jami’an hukumar NDLEA da ke aiki a filin jirgin saman Akanu Ibiam da ke Enugu da masu aiki a tashar jirgin ruwa na Tican da ke Legas sun samu nasarar daƙile yunƙurin shigo da kilogiram 126.95 na hodar ibilis da tabar wiwi ƙunshe cikin ƙwalayen ganyen shayi da ababen hawa daga Brazil da Canada”.

Sanarwar ta ƙara da cewa a filin jirgin saman Enugu an kama wani fasinja mai suna Eze Christian Ikenna mai shekara 42, da ya shiga ƙasar daga Brazil ranar 20 ga watan Janairun, bayan da aka binciki jakar da ya zo da ita inda ka samu hodar ibilis da ta kai nauyin kiligiram 16.2.

PRNigeria hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp